Ana ce-ce-ku-ce da cacar-baki a kan maƙudan kuɗaɗen da Buhari ya shigar a kasafin 2022, domin kashewa wajen gina sabon Asibiti Sashen Shugaban Ƙasa a Fadar Aso Rock, wanda za a kashe wa Naira biliyan 21.9.
Asibitin dai idan an kammala shi nan da shekara biyu, zai riƙa kula da Shugaban Ƙasa da iyalin sa, Mataimakin Shugaban Ƙasa da iyalin sa, sai kuma sauran manyan ƙusoshin gwamnatin tarayya.
Babban abin damuwa dangane da waɗannan maƙudan kuɗaɗen da za a kashe, shi ne ganin yadda idan an haɗa kuɗaɗen da Buhari zai kashe a Manyan Asibitocin Najeriya 14, wato Federal Teaching Hospital, ba su ma kai adadin waɗanda za a kashe a asibitin Fadar Shugaban Ƙasa ba.
Wannan ya janyo ana kukan cewa Buhari bai damu da inganta rayuwar ‘yan Najeriya ba.
Sannan kuma ana kukan yadda kasafin bai bada fifiko ga harkokin ilmi da kiwon lafiya ɗungurugum ba.
Da wahala wannan asibiti da za a gina a Fadar Shugaban Ƙasa ya zama dalilin daina fitar Buhari zuwa Landan, domin duba lafiyar sa. Saboda sai nan da shekaru biyu za a kammala ginin, wanda a lokacin ki dai Buhari ya fara yin bankwana da kujerar mulki, ko kuma ya kammala ya koma Daura da zama.
Kafin Buhari ya nemi amincewar Majalisar Dattawa da ta Tarayya domin kashe Naira biliyan 21.9 wajen gina asibiti a cikin Fadar sa, a shekarar da ta gabata an kashe Naira biliyan 1.4 a wajen aikin asibitin.
Babban Sakataren Fadar Shugaban Ƙasa, Usman Tijjani ya bayyana wa sanatocin da su ka kai ziyara asibitin a cikin Agusta cewa, idan aka kammala shi, zai kasance manyan jami’an gwamnati da iyalan shugaban ƙasa da na mataimakin sa da su kan su Shugaba da Mataimaki, duk a wurin za a riƙa duba lafiyar su.
Wannan kasafin asibitin fadar Buhari ya haura na manyan asibitocin Najeriya 14 (Federal Teaching Hospitals) yawa da Naira biliyan 2.7 kenan.
Discussion about this post