Shugaba Muhammadu Buhari ya bayyana cewa bashin da gwamnatin sa ke ciwowa bai kumbura cikin da zai rikita ƙasar nan ba.
Ya ce ayyukan da ake yi da kudaden da ake ciwowa bashi a bayyane su ke, don haka duk mai tantama zai iya fita ya yi bincike ya gani da kan sa.
Buhari ya yi wannan kalami a gaban gamayyar Sanatoci da Mambobin Majalisar Dattawa, yayin da ya ke gabatar masu da kasafin 2022 na Naira tiriliyan 16.39.
A cikin kasafin dai ya bayyana cewa Naira tiriliyan 4.11 za a kashe su wajen biyan albashi da sauran haƙƙin tafiyar da ma’aikatan gwamnati.
Sai kuma zunzurutun Naira tiriliyan 3.61 waɗanda za su tafi wajen biyan basussukan baya, wanda gwamnati ke yi a kowane ƙarshen wata.
Buhari ya ce za a kashe Naira biliyan 579 wajen biyan haƙƙin ‘yan fansho da biyan garatuti.
Yayin da Buhari ke jawabi, ya yi bitar wasu muhimman ayyukan da gwamnatin sa ta yi a shekarar da ta gabata, sannan kuma ya jinjina wa kan sa bisa ƙoƙarin da ya yi na tsayuwar sama da minti 50 ya na jawabi wajen gabatar da kasafin 2020. Kuma ya ce a wannan ranar ma zai yi bajintar sake yin irin waccan tsayuwar.
Buhari ya gabatar da Kasafin kudin 2022 ga yan majalisun tarayya taran Alhamis.
Discussion about this post