Tabbas a bin maraba ne yunkurin da Yan Majalissun Tarayya suka yi na sake gyara dokar zabe ta 2021, musamman ma sanya Jama’iyyu yin zaben Primary Election ta hanyar Yar-Tin-Kai wato Direct Primary.
Wannan zai ba wa ‘yan Jama’iyya damar tantancewa wajen zaben dan takarar su, sabanin yi musu kakabe da sunan sasanto ko amafani da wasu mutane kalilan da sunan wakilai wato delegate.
Yana daga cikin burin kowane dan kasa a dimokkaradiyya samun damar zaben shugabbannin da suke so su jagoran ce su, musamman ma a yi dacen samun nagartattu shugabannin wayanda suke kishi da jajircewa a kan manufar ciyar da kasa gaba.
Ingantanccen mulki ne kadai ke iya fidda kowace kasa daga kangin koma baya zuwa tafarkin ci gaba ta hanyar habaka tattalin arzikin kasar ta kowa ne fanni, wanda hakan ne kadai zai iya maganin talauchi da zama irin na kiki juna, za a sami sukunin bunkasa ilimi, lafiya da kuma tsaro.
Nijeriya tun dawowar ta mulkin dimokaradiyya take fama da rashin ingancin shugabanci da shugabbanni, wanda a ko da yaushe ke barazanar wargajewar kasar, zamu iya tabbatar da hakan wajen yadda harkar tsaro da tattalin arziki suke lalace tun dawo war kasar nan tafarkin dimokaradiyya, ga zama irin na kiki juna, musamman ma a wadan nan shekaru.
Ko da a wannan shekarar ma Nijeriya ce kasa ta 102 da cikin kasashen duniya 104 wajen rashin ingancin shugabanci, kamar yadda kididdigar hukumar Chandler Good Governance Index (CGGI) ta fitar, wanda Nijeriya ta samu sakamako 0.319 point, wanda da kadan ta wuce kasar Zimbabwe da Venezuela.
Nijeriya na fama koma bayan ita kan ta dimokaradiyyar, ta yadda mutane kalilan, musamman wayanda suka samu damar dafe mukammai a kasar ke juya siyasar yadda suke so, sun maida yin takara ga kawai mutanen da suke so, babu la’akari da kwarewa ko chanchanta ko ma siyasar. A wuni bigiren ma ana son a maida siyasa tamkar kayan gado ko nadin sarauta.
Dimokaradiyya kan samu inganci ne kawai, in har an samu ingantttun jama’iyyu, masu agida da manufa da za su iya gogayya da juna.
Jama’iyyun siyasa, su suka fi kowa ruwa da tsaki wajen zakulo yan takarkarun da suke da inganci wajen jan ragamar kasar nan ta hanyar shugaban ci a dukka nin matakai.
Ruf da ciki ko mallake jam’iyyun siyasa daga kalilan din mutanen da suka samu dama ta mulki, ya sanya dukkanin manyan Jama’iyyun kasar nan suke cikin rigima da rudani, musamman na shugabanci, da kokuwar kowa ya dora nasa a kan mulki ko yin takara.
Yawan canja sheka da manyan yan siyasar kasar nan ya kara kashe karkashin dimokaradiyyar, da kuma rusa imanin yan kasa wajen yiyuwar samun shugabanci da shugabanni na gari.
A yau babu wata jaha da ba za a samu cece-kuce ba tsakanin gwamna da wasu zabbabbun ko masu mukami irin su Sanata, Reps ko Minista, wanda wannan ke nuna rashin ingancin siyasar cikin jama’iyya.
Kamar yadda na fada, jama’iyya ke da babbar dama ta fidda ingantattun shugabanni, domin ta jama’iyya kawai za a iya yin takara ko wacce iriya ce domin hawa kan mulki. Saboda da haka ingancin yin Primary election yana da tasiri wajen samun ingantattun shugabanni.
Mutane da dama suna ganin tsarin fidda ya takara ta delegate ko sasanto kawai yana bawa masu iko ne bawa mutanen da suka ga dama tikitin yin takara, walau sun cancanta ko basu cancanta ta ba, walau a na son so ko akasin haka.
Gyaran dokar zaben da Majalissar Dattijai tayi na gyara yadda za a fittar da wayanda za su yi wa jama’iyya takara abin maraba ne kuma zai dawo da kyakkyawan zaton samun shugabanni na gari.
Majalissar Dattijai ta gyara Sashe na 87 (1) na dokar, wanda yake umarnin Jama’iyyu su gudanar da zaben yan takarar da suke so a a zabe ta hanyar Yar-Tin-Kai wato Direct Primaries , bisa sanya idon hukumar zabe ta kasa. Kudurin da Sanate leader Senator Abdullahi Yahaya ya gabatar.
Wanann gyaran ba kawai zai dawo wa yan jama’iyya yarda da cewa za su iya zaben yan takarar da suke so ba ne kawai, wannan kan iya gyara su kansu jama’iyyun wajen yin siyasa da yawun mutanen su.
Haka zalika wannan gyara zai iya rage babakeran da masu mulki sukayi, musamman ma zabbabu a kan wadan nan jama’iyyu, kuma zai bada damar nagartattun mutane shigowa a dama da su a siyasar.
Tabbas kawai ingantancen mulkin da jama’a suka zaba ne kadai zai kai dimokaradiyyar mu gaci.
alhajilallah@gmail.com
Discussion about this post