• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe – Nazarin DUBAWA

    INEC ba za ta rufe rajistar zaɓen 2023 a ƙarshen Yuni ba – Farfesa Yakubu

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe – Nazarin DUBAWA

    INEC ba za ta rufe rajistar zaɓen 2023 a ƙarshen Yuni ba – Farfesa Yakubu

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

BINCIKEN ‘Pandora Papers’: Hukumar Tara Kuɗaɗen Haraji za ta bi waɗanda aka lissafa sun karya dokar biyan haraji

Mohammed LerebyMohammed Lere
October 8, 2021
in Labarai
0
Federal Inland Revenue Service

Federal Inland Revenue Service

Hukumar Tara Kuɗaɗen Haraji ta Ƙasa (FIRS) ta bayyana cewa za ta bi diddigi ta hukunta dukkan ‘yan Najeriya da aka kama sun karya dokar biyan haraji a cikin harƙallar ‘Pandora Papers.’

Cikin wata sanarwa da Kakakin FIRS Johaness Woluola ya fitar, ya ce hukumar za ta bi dukkan mutanen da lissafa sun karya dokokin biyan haraji domin a hukunta su.

Daga cikin ‘yan Najeriya da aka rigaya aka lissafa dai akwai tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi, Gwamnan Kebbi Abubakar Bagudu, Sanata Stella Oduah, Shugaban Riƙo na Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa, Bello Koko da Gwamna Gboyega Oyetola na jihar Osun da kuma makusantan su.

PREMIUM TIMES za ta ci gaba da fallasa sauran, da ya ke su na da yawan gaske.

PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin yadda Bello Koko ya daɗe ya na takarar saye gidaje da kadarorin birnin Landan har a gwamnatin Buhari.

Yawancin masu karatu ba su san Mohammed Bello-Koko ba. Amma ɗan taƙaitaccen ƙarin bayanin da za a yi yanzu a kan sa, zai sa kowa ya gane cewa lallai ‘biri ya yi kama da mutum.’

Bello Koko shi ne ma’aikacin gwamnatin da Shugaba Muhammadu Buhari ya amince da naɗa shi riƙon Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa (NPA), bayan cire Hadiza Bala Usman.

Shugaban Riƙon Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa na Najeriya (NPA) Bello Koko, ya shiga cikin ƙazamar ƙamayamaya da ƙaƙububar satar kuɗaɗen Najeriya ya na kartatar da su waje, inda ya ke sayen maka-makan gine-gine da kadarori a birnin Landan.

A ƙarƙashin wannan harƙalla, ya riƙa yin shigar kare-da-fatar-akuya da sunan wasu kamfanoni biyu na Shell, ya riƙa danƙara kuɗaɗen da ake sayen kadarori a Landan.

Gungun ‘yan jarida masu yaƙi Da ɓarayin kuɗaɗen gwamnati a duniya ne su ka bankaɗo wannan ƙazamar harƙallar da ake kira ‘Pandora Papers’.

Bello Koko tare da matar sa mai suna Agatha Anne Koko, sun yi amfani da wani kamfanin ɓoye sirrin maɓarnata, Cook Worldwide and Alemin, su ka yi rajistar kamfani a asirce ta hanyar ɓoye sunayen su, aka sa sunayen bige a matsayin masu kamfanin.

An raɗa wa kamfanin suna Coulwood Limited, mai rajista lamba 1487897.

An sake ƙirƙirar wani kamfanin na bige mai suna Marney Limited a British Virgin Islands, mai lamba 1487944, duk a cikin 2008.

Waɗannan kamfanonin biyu an yi masu rajista duk a rana ɗaya, 19 Ga Yuni, 2008.

Duk da Bello Koko ma’aikacin gwamnati ne, ya kasance daraktan kamfanonin, abin da ya saɓa wa Dokar Aikin Gwamnanti a Najeriya, Sashe na 5 da na 6.

Harƙallar Bello na daga cikin harƙalla miliyan 11.9 da Gamayyar Ƙungiyoyin ‘Yan Jaridar Binciken Ƙwaƙwaf na Duniya (ICIJ) su ke ci gaba da fallasawa bayan sun bankaɗo su.

Jaridar PREMIUM TIMES kaɗai ce cikin wannan ƙungiya a jaridun Najeriya. Kungiyar ta ƙunshi ‘yan jarida 617 daga gidajen jaridu 150 na ƙasashen duniya.

Waɗannan ‘yan jarida sun shafe shekaru biyu su na bicike a cikin harƙallar tare da bin diddigin hanyoyin da ake satar kuɗaɗen, binciko fayil-fayil ɗin wasu shari’un da ake yi na wasu ƙasashe daban-daban.

Wannan fallasar manyan ɓarayin gwamnati ita ce mafi girma da ‘yan jarida su ka taɓa yi daga cikin ƙasashe 117 na duniya.

Kadarorin Da Bello Koko Ya Saya Cikin Landan, A Ƙarƙashin Mulkin Buhari:

Daga cikin kadarorin da Bello Koko ya saya Landan, har da waɗanda ya saya a Landan cikin 2017, lokacin da bai daɗe da zama Babban Darakta a NPA ba.

Sauran kadarorin kuma ya saye su tsakanin 2008 zuwa 2012.

Da farko ya sayi gida mai Lamba 2, Liberty Court, 141, Great North Way, London.

Ya sayi gidan a ranar 20 Ga Okotoba, 2009, ta hannun dillalin FBN UK mortgage.

Ranar 23 Ga Yuli, 2012, ya sayi mai Lamba 62, Manton Road, Enfield, London.

An sayi ɗaya fam 280,000, ɗayan kuma fam 275,000.

Bello Koko ya sake amfani da kamfanin Coulwood a wannan karo, ya sake sayen gidaje uku.

Akwai mai Lamba 62 Corner Mead, Hendon, (NW9 5RD) a ranar 25 Ga Nuwamba, 2008.

Sai gida mai Lamba 37, Redlands Road, Elfield da aka saya a ranar 16 Ga Agusta, 2011.

Lamba 14, Farady House, Aurora Garden, London, shi kuma an saye shi a ranar 3 Ga Mayu, 2017, a wannan gwamnati ta Mahammadu Buhari.

Na farkon an biya fam 205,000, sai na biyu fam 235,000. Sai kuma gidan Hendon da ya biya fam 350,000.

Na Aurora Garden kuwa da ya saya cikin 2017, ya biya lakadan fam 475,000.

Wannan kantamemen gini shi ne babbar kadara mafi girma da Bello Koko ya saya a Landan.

Kuma ya saye ta lokacin mulkin Buhari ɗin nan, ya na aiki a Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa (NPA).

Kamfanonin harƙallar Bello Koko na cikin waɗanda Hukumar Bibiyar Harƙalla a Birtaniya (FIA) ta kafa wa idon mikiya a halin yanzu.

Kafin Bello Koko ya fara aiki a Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa, ya kashe fam miliyan 995,000 wajen sayen kadarori a Landan, tsakanin 2008 zuwa 2012 kenan.

Ba a san dalilin da ya sa ya riƙa sayen gidajen da sunan bogi, maimakon sunan sa na gaskiya ba.

PREMIUM TIMES ta aika masa da saƙon tes, domin jin ta bakin sa, har yau bai maido amsa ba.

A ranar 27 Ga Janairu, 2017, Hukumar Binciken Kuɗaɗen Harƙalla (FIA) a Landan ta nemi ƙarin bayanai dangane da ganin sunaye da kuma bayyanar masu kamfanonin da Bello Koko ke harƙalla, tare da neman wasu ƙarin bayanai daga gare su, amma aka yi ta dawurwura da dabur-dabur.

Tags: AbujaHarajiHausaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

BINCIKEN ‘Pandora Papers’: Yadda Gwamnan Osun Oyetola ya sayi gidan fam miliyan 11.95 a Landan

Next Post

Ƴan shaye-shaye sun cinna wa taragon Jirgin Kasa biyu wuta a jihar Kwara

Next Post
Ƴan shaye-shaye sun cinna wa taragon Jirgin Kasa biyu wuta a jihar Kwara

Ƴan shaye-shaye sun cinna wa taragon Jirgin Kasa biyu wuta a jihar Kwara

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • FARGAR JAJI: Zamfara ta kafa Hukumar Tsaron Jama’a
  • ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC
  • Ka zo ka yi mini mataimaki kawai – Kwankwaso ga Peter Obi
  • RIKICIN KWANCE WA ATIKU ZANI A KASUWA: Rundunar PDP ɓangaren Wike sun nemi a tsige Ayu, Shugaban Jam’iyya
  • YADDA KALLO YA KOMA OGUN: Obasanjo ya karaɗe Abeokuta ya na ɗaukar fasinja da Keke NAPEP

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.