Jami’in hulda da jama’a a sashen yi wa mutane allurar rigakafi na jihar Legas Kolawole Oyenuga ya yi kira ga gwamnatocin jihohin kasar nan da su rika raba abinci a wuraren da ake yin allurar rigakafin korona idan suna son mutane su rika fitowa ana yi musu rigafin korona babu cikas.
Oyenuga dake aiki a cibiyar lafiya a matakin farko dake Ikorodu ya yi wannan kira ne da yake ganawa da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN a garin Legas.
Jami’in ya kara da cewa baya ga tsoro samun matsala kila idan anyi allurar, akwai rashin kwanciyar hankali da matsalolin rashi da talauci da ke damun mutane wanda bashi allurar bane a gabansu, abinda za a saka a abaki ne ya fi damun su.
“Idan har mutane suka san idan za su samu lafci tuwo a wurin yin rigakafin korona, za su rika tururuwa suna fitowa domin ayi musu rigakafi.
Oyenuga ya yi kira ga gwamnati da ta kara himma wajen wayar da kan mutane sanin mahimmancin yin allurar rigakafin Korona.
Yaduwar cutar
Legas – 76,930, Abuja-22,140, Rivers-12,233, Kaduna-9,718, Filato-9,445, Oyo-8,701, Edo-6,502, Ogun-5,332, Kano-4,200, Akwa-ibom-7,336, Ondo-3,968, Kwara-3,871, Delta-3,494, Osun-2,818, Enugu-2,675, Nasarawa-2,458, Gombe-2,333, Katsina-2,212, Ebonyi-2,048, Anambra-2,346, Abia-1,975, Imo-1,937, Bauchi-1,617, Ekiti-1,736, Benue-1,679, Barno-1,344, Adamawa-1,136, Taraba-1,074, Bayelsa-1,125, Niger-968, Sokoto-796, Jigawa-587, Yobe-501, Cross-Rivers-587, Kebbi-458, Zamfara-253, da Kogi-5.