Tsohon Gwamnan Jihar Imo, kuma Sanatan Imo ta Yamma, Rochas Okorocha, ya bayyana cewa babu wani dalilin da zai sa Jam’iyyar APC ta ƙi damƙa takarar zaɓen shugaban ƙasa a 2023 a hannun yankin Kudu maso Gabas.
Okorocha ya yi wannan furuci ne ranar Litinin a Abuja, a yayin taron ganawa da manema labarai, a Hedikwatar Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ), a Abuja.
Ya ce tabbas akwai yarjejeniyar da ba rubutacciya ba a APC cewa za a riƙa yin mulkin karɓa-karɓa. Kuma a yanzu lokaci ne da idan dai adalci za a yi, to a yankin Kudu maso Gabas ɗan takarar shugaban ƙasa na APC ya kamata ya fito.”
Rochas ya ce tabbas ana maida ƙabilar Igbo saniyar-ware a wannan gwamnati, amma ba wannan ne abin damuwar ba.
“Magana a yanzu ita ce kowane yanki ya yi shugabanci kuma an ga kamun ludayin su. Don haka a yi adalci a miƙa mulki a hannun ƙabilar Igbo, domin shi ma a ga na sa kamun ludayin.”
Rajin Rochas Okorocha ya zo ne kwanaki kaɗan bayan Sanata Abdullahi Adamu na Jihar Nasarawa ya ce kada a bi tsarin karɓa-karɓa, a bi cancanta kawai ko ma daga ina a ɗauko ɗan takarar APC.
Sai dai kuma kwata-kwata Rochas bai yarda da ra’ayin sa ba.
“Idan aka ce za a sake fito da ɗan takara daga Arewa, ai kuwa za a samu ɓaraka a APC, domin sauran yankuna za su yi mata kallon jam’iyyar ‘yan Arewa zalla.”
Tuni dai a jam’iyyar APC tafiya ta yi nisa wajen tallata jagoran jam’iyyar, Bola Tinubu.
A gefe ɗaya kuma wata ƙungiyar CPG ta bayyana, mai hanƙoron ganin Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo ya maye gurbin Shugaba Buhari a zaɓen 2023.
Discussion about this post