Gwamnan Kaduna, Nasir El- Rufai ya yi kira ga ƴan Kaduna da su gaggauta fita zuwa wuraren zaɓe domin Kaɗa kuri’ar su ga ƴan takarar su.
El-Rufai ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi da ƴan jarida bayan ya kaɗa kuri’ar sa a zaɓen ƙananan hukumomin Kaduna.
” Ni na jefa tawa ƙuri’ar kuma abin zassauki. Tantancewar ta fi kaɗa ƙuri’ar wahala ma saboda saukin na’urar zaɓe da muka yi amfani da su.
Discussion about this post