• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Jami’o’in Najeriya da Kalubalen kirkira da samar da kwararru, Daga Ahmed Ilallah

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
September 23, 2021
in Ra'ayi
0
Jami’o’in Najeriya da Kalubalen kirkira da samar da kwararru, Daga Ahmed Ilallah

Ahmed Ilallah

Tabbas Nijeriya ta samu kanta a wani yanayi a cikin wannan shekaru, banda abin da ya fito a zahiri na talauchi da karayar tattalin arziki kama da bullowar ta’adanci da sunan addini a arewacin Nijeriya wanda ya haifar da kungiyoyin ta’adda irin su Boko Haram, ISWAF, kaluballe na ‘Yan-fashin Daji, Satar Mutane don biyan Kudin fansa. Wanzuwa da kungiyoyin bore irin su IPOB, Oduwa Republic, karuwar masu zamba ta hanyar internet (Fraudsters) wand yafi tasiri a kukdancin Nijeriya. Wadannan matsalolin sun dau rayukan dubban yan Nijeriya, sun sanya miliyon yan kasar rabuwa da muhallan su, sun raba iyalai da dama, rabuwa ta har abada, hakan ya kawo koma baya mutuka a wajen ilimi, kiwon lafiya da zamantakewa.

Gurbacewa da lalacewar siyasa da mulkin dimokaradiyya, bunkasa da sabon salon almundahana, cin hanci da rashawa a wannan kasar kadai, ya isa muyi karatun tanutsu, kullum Nijeriya tana cikin kasashe koma baya a duniya wajen ingantancen mulki da cigaban dimokaradiya, talauchi da koma bayan tattalin arziki, shugabanni sun gaza samar da mafita.

Musani fa ita kanta Dimokaridyyar da salon yadda ake gudanar da it bincike ne na masana da jami’io ya samar da ita, kuma kullun bibiya ake bisa ilimi na al’ummah na zahiri don kara inganta ta da kawo sauyin da ya dace da yanayin da aka samu kai.

Amma fa musani duk wadannan matsalolin magance su ya wuce kawai yin yaki ko hukunta su a gaban kuliya dole sai an bawa kwararrun mu dama sun binciko musabbabin aukuwarsu, ruruwarsu dama yadda ake kitsa su, domin ta haka ne kawai za a iya maganinsu har abada a kuma dora Nijeriya a bigiren cigaba.

Tabbas cigaban kowace kasa a duniya ya ta’allaka da kokarin kasar na cin ribar ilimin da take samarwa yan kasarta, mu samman a wannan zamanin na gudun yada kanin wani, bisa doron da cigaban kimiya da fasaha ya dora duniya a kai, musamman fasahar sadarwa ta zamani (ICT).
Jami’a dama manyan makarantu ba kawai anyi su bane don koyo da koyarwa ba ko bada kwalin digiri ko diploma ba kadai. Jami’a wurin ne na koyo da koyarwa da kuma bincike, yayin da binciken da aka gudanar, a kan shigo da shi don bunkasa rayuwar al’umma, kasa da duniya baki daya.

Duk cigaban da ake gani a duniya na kowane fanni daga kere-kere, fasahar tattalin arziki, noman zamani, zaman lafiya da dabarun yaki ana samar da sune ta hanyar bincike, wanda akasari a kan yi su a Jami’a ko manyan makarantu.

Farau din fasahar sadarwa ta zamani wato computer an kirkiro tane a Manchester University a shekarar 1948 daga kwararrun masu ilimin kimiya Freddie Williams da abokin aikin sa Tom Kilburn. Mark 1, injin da ke gani har hanji wato (scanning machine), an kirkire shine a University of Aberdeen. Magani mai yaki da cutukan bacteria wato Penicillin an fara kirkirarsa ne a University of Sheffield a 1930. Duka wannan yana daga aikin bincike da ake gudanarwa a Jami’oi da manyan makarantu.

Fasahar Web Browser da Talabijin din zamani ta Bango (Plasma Screen) an kirkira ne a University of Illinois ta kasar Amurka, haka zalika fasahar injin bincike na sadarwar zamani wato google an bincikota ne da kirkirar sa a Stanford University, wanda a yau kasafin kudin (Budget) kamfanin Google, yafi girman Kasafin kudin Nigeria. Jahar California ta kasar Amurka tana daga cikin masu karfin tattalin arziki a duniya, tana samun kudin shiga akasari daga amafanin bincike na fasaha da ga Stanford University dake jaharta ta hanyar cusa binciken cikin harkokin kasuwaci da tattalin arziki.

A duniyar yau magana ake ta artificial intelligence, robotic, block chain, biosensors, 5G da sauran su, wanda kusan da wadannan kirkiru ne ake daura kinshikin gina tattallin arzikiki da bunkasar sa. A yau kamfanin sadarwa irin su Microsft Facebook, Twitter da sauransu suna da karfin arzikin da yafi kasashen Africa da dama.

Duk wannan fasahar an kirkiro su ne bisa bincike da akeyi a Jami’oi da manyan makarantu na kasashen turai musamman ma Amurika.

Ba wai kawai bincike na zahirin kimiya ba hatta bincike na zamantakewar Dan-adam, da yadda kasa zata zauna lafiya, da yadda kasa zata bunkasa tattalin arzikinta, bincike na dabarun yaki da kare kai da duk wani fanni na rayuwar al’ummah duka a kasashen da aka ci gaba ana gudanar dasu ne a manyan makarantu da Jami’oi, wannan ya sanya dangantakar gown da town ta ke da mutukar muhimmanci a Jami’a.

Amma fa Jami’oin Nijeriya da shehunan malamai da dalibai suna cikin sukunin yin bincike da zaiyi tasiri kamar haka? Kamun ludayin da aka yi wa ilimin manyan makarantu a Nijeriya yayi munin da ba zai haifar da da mai ido ba harma ya fidda kitse da ga rogo, wannan matsalolin a zahirance suke.

ASUU da gwamnatin tarrayya dama sauran ma’aikatan Jami’a irin SSANU sun kasa kai gaci wajen samun tabbataciyar matsaya akan ilimin jami’oin, haka zalika Malaman da ma’aikatan manyan makarantun kasar nan, a wani zangon, tsawon yajin aiki da ake yi yafi lokacin karatun da ake yi, balle a samu lokacin bicike na dunbin matsalolin kasarnan.

A Nijeriya ne ake biyan Professor albashin kasa da $1,000, ga kuma jibgin aiki na koyo da koyarwa akan sa, sannan a tsammaci kyakkywan tunani a wajensa na yin bincike da kirkira. Wanda a fagen ilimi wanann albashin yayi kadan bisa yanayin tsadar rayuwar Nijeriya. Talauchi babban tasgaro ne a harkar ilimi.

Jami’oin Nijeriya suna cikin mummnan hali na rashin gine-gine na dole don koyo, koyarwa da binchike, dakin gwaje-gwaje (laboratories) abin takaici ne, kai hatta ruwan sha, wutar lantarki, wurin kwanan dalibai, dakunan daukan karatu duka suna cikin mummunan yanayi, balantana offisoshin malamai. Yunkurin ayi gyara ya sanaya ake ganin rigimar kungiyoyin nan da gwamnati ta gagara karewa.

Banda gamagarin matsalolin da suka sahafi manyan makarantun mu, shi kansa kudin da ake warewa don Binciken (Research Grant) yayi kadan mutukka. Hukumar kasa ta TETFund wanda take da alhakin tattara kudaden haraji na ilimi daga kamfanoni ke biya don rabashi ga manyan makarantu na kasa, a baya ta kan ware Naira Bilayan Uku kachal (N3B), amma wannan gwamnatin ta kara zuwa N7.5B, wanda wannan kason yayi kadan mutuka in har ana son kwalliya ta biya kudin sabulu. Tsohon shugaban hukumar jami’oi ta kasa (NUC) Professor P. Okebukola yayi nuni da cewa N7.5B yayi kadan mutuka, wannan kason da ake warewa bai kai yawan wanda ake ba kananan masu bincike ba na MIT da Harvard.

Sannin kanmu ne Allah ya yiwa Nijeriya baiwa da masu ilimi, bincike da aiki tukuru, amma samun dama da kuma kudaden yin wannan binciken duk da kasancewar wani lokacin akan samu gudunmawa da ga wasu hukumin masu zaman kansu ko kamfanoni.

Kamar yadda samun gudunmawar Bincike akwai na gida da kuma waje (wato hukumomin kasashen duniya), wanda wannan shi yafi wahalar samu a wajen malaman jami’oin misali a yan shekarun baya, wasu Malaman Jami’ar Legas (UNILAG) sun sami tallafi na bincike (Research Grant) daga hukumomin kasashen wajen kimanin N12B.

Rashin ganin tasirin bincike da manyan makarantun mu a zahirance, ke sanya shakkun yi ko ingancin binciken ko kuma rashin amfani da shugabanni basa yi akan binciken. Wai shin me ka faruwa ne a kasar mu wajen ganin tasirin irin wadannan binciken da makamantan su don raya kasarmu. Shin Shehunnnan Malaman mu a Jami’a basa kirkira ne ko bincike? Ko kuma binciken baya shigowa cikin al’umma? A’a shugabannin kasarne ba sa bawa wannan bangare muhinmanci?

Koda an samu amsoshin wadannan tambayoyi, to tabbasa akwai tazara ta masu mulki da bangaren ilimi. Dalilai da dama sun nuna shugabbannin Nijeriya suna jagorancin tane ba akan doron ilimi ba, ko kuma yiwa mulkin gangancin don rashin kishin kasa ta yadda zamu bawa wannan fanni muhimmanci kamar kowace kasa mai son ci gaba a duniya.

A kullum ana kashe magudan kudade don hayar kwararru daga kasashen ketere, wanda za’a iya samar da su a gida, in har an inganta koyo, koyarwa da bincike a manyan makarantun mu. Duk dinbin jami’oin mu, har yanzu bamu daina shigo da irin shukawa a gona ba, bamu daina shigo kayan da zamu iya ganoshi da ingantashi a kasar mu ba.

Duk kasar da ta kasa bincike da samo maslaha kan al’amuran cigabanta da matsalolin dake damun al’umarta, tabbas an barta a baya, kuma talauchi zaichi gaba da mata kawanya tunda babu dabaru na ilimi wajen yaye wannan matsaloli.

alhajilallah@gmail.com

Tags: AbujaHausaKwararruLabaraiMakarantaMakarantuNajeriyaPREMIUM TIMES
Previous Post

Kaso 80 na ‘yan siyasar Najeriya suna canja jam’iyya ne don bukatarsu, Daga Mustapha Soron Dinki

Next Post

MUSULUNCI A KASAR INYAMIRAI: Yadda ba a dauke mu mutane ba, wulakancin yau da ban da na gobe – Malam Okonkwo

Next Post
MUSULUNCI A KASAR INYAMIRAI: Yadda ba a dauke mu mutane ba, wulakancin yau da ban da na gobe – Malam Okonkwo

MUSULUNCI A KASAR INYAMIRAI: Yadda ba a dauke mu mutane ba, wulakancin yau da ban da na gobe - Malam Okonkwo

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Takardun sakandare na sun yi layar-zana, amma ina da sakamako mafi kyau -Okowa, mataimakin takarar Atiku
  • HAJJIN BANA: Hankulan maniyyatan Kano 1,238 ya tashi saboda kasa kwashe su kan lokacin rufe filin jirgi Jeddah
  • IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi
  • 2023: Ka zaɓi El-Rufai mataimaki, ‘ka yi nasara a zaɓe kamar yankan wuka’ – Kira ga Tinubu
  • RIKICIN PDP: Kwamitin Amintattun PDP ya tura wa Wike tawagar lallashi

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.