• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan da ya kamata a sani game da allurar rigakafin COVID-19, guda ukun da aka shigo da su Najeriya – Binciken DUBAWA

Silas JonathanbySilas Jonathan
September 3, 2021
in Kiwon Lafiya
0
Najeriya za ta karbi kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona miliyan 41 a karshen Satumba  – Inji Shu’aib

Ranar 2 ga watan Maris 2021 Najeriya ta zama kasa ta uku a cikin jerin kasashen da suka karbi allurai miliyan hudu na Oxford/ AstraZenece a yankin yammacin Afirka, bayan kasashen Ghana da Ivory Coast, ta hannun COVAX ko kuma gidauniyar kasa da kasa ta samar da allurar rigakafin COVID-19.

Kawo yanzu gwamnatin Najeriya ta ce ta yi amfani da milliyan 3.97 na AstraZeneca a yayinda mutane miliyan 1.42 kuma sun karbi allurar a kasar baki daya.

Ba da dadewa ba gwamnatin Najeriya ta sake samun wasu alluran miliyan hudu na Moderna a matsayin gudunmawa daga Amurka, don taya kasar yaki da zagaye na uku na barkewar cutar. Hukumar UNICEF ce ta karbi wadannan allurai a madadin Najeriya. Alluran sun sauka a Abuja tashar jirgin saman Nnamdi Azikiwe a jirage biyu.

Bayan nan, kasar ta sake samun wasu karin 177,600 na Johnson & Johnson, shi kuma ta hannun kungiyar Tarayyar Afirka wato AU a ranar 12 ga watan Agusta 2021.

Hukumar NPHCDA, wadda ke tabbatar da cigaban kiwon lafiya a matakin farko na al’umma ta ce wannan adadin, rukunin farko ne da kungiyar ta AU kuma za’a cigaba da karbar magungunan kowane wata har sai an sami miliyan 29.8 wanda shi ne cikakken adadin da aka alkawarta mata.

Cikakken bayani kan kowace allura

Allurar Oxford-AstraZeneca kwayar cutar ce da aka kirkiro a jami’ar Oxford tare da taimakon kamfanin magunguna na AstraZeneca ke cikin allurar da ake bayarwa. A cewar Medical News Today, jaridar da ke bincike da rubutun batutuwan da suka shafi kiwon lafiya, ta ce wannan kwayar cutar na dauke da wasu kwayoyin halitta da ke kwaikwayon nau’in abincin da ake kira furotin ko protein a turance, wanda aka saba gani a saman kwayar cutar SARS-CoV-2. Da zarar ta shiga jikin mutun, kwayoyin halittan kan sanya wasu kwayoyin jikin su fara sarrafa protein. Kasancewar wannan nau’i na protein ne ke taimakawa jiki ya fara sarrafa kwayoyin da za su inganta garkuwan jikin mutun wajen yakar cutar COVID-19 ko da ya shiga jikin. Allurar ta na da wa’adin watanni shidda ne kadai idan aka sa fridge mai sanyin digiri 2 zuwa 8 bisa ma’aunin Selshiyus. Idan har aka cire daga cikin fridge ana iya ajiye ta a wurin da ke da sanyin digiri 2 zuwa 25 a ma’aunin selshiyus na tsawon sa’o’i shidda ne kadai.

Allurar Moderna an yi mata lakabi da suna mRNA-1273 kuma kamfanin Moderna ya sarrafa, tare da Cibiyar kasa ta nazarin rashin lafiya da cututtuka masu saurin yaduwa na Amurka (NIAID) da hukumar bincike da tattabar da ci-gaban illimin halitta (BARDA). Allurar rigakafin Moderna allurar da aka fi sani da mRNA ce wato kwayar halittar da ake sarrafawa, wadda ke baiwa jikin umurnin sarrafa sinadarin da ake kira spike protein ya kuma koya wa jikin yadda zai iya gane shi. Da zarar aka yi haka garkuwan jikin mutun zai fara yakar spike protein a duk sadda ya gan shi. A cewar kamfain allurar tana da karfin yakar cutar da kashi 90 cikin 100 kuma a lokutan da cutar ta ke da tsanani, karfin yakar na iya kaiwa har kashi 95 cikin 100, idan aka kara yin allurar watanni shidda bayan da aka karbi kashi na biyu.

Johnson & Johnson ce allura ta uku wadda Hukumar kula da abinci da magunguna na Amirka ta amince a yi amfani da ita a mataki na gaggawa wajen magance cutar a jikin mutun, bayan Pfizer da Moderna. Ko da shi ya banbanta kadan daga Pfizer da Moderna, domin Johnson & Johnson ya fi kama da Oxford-AstraZeneca tunda su sun yi amfani da kwayar cutar ne mara lahani wajen aikar da irin umurnin da jiki ke bukata dan gini garkuwar jiki.

Banbancin Oxford-AstraZeneca, Moderna da Johnson & Johnson

Banbancin da ke tsakanin Moderna, da Johnson and Johnson da AstraZeneca ba yawa, kuma su ne allurai ukun da aka kawo Najeriya. Duk ukun kuma Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta amince a yi amfani da su a lokacin da ake bukata da gaggawa, ita ma hukumar NAFDAC ta amince da hakan.

Oxford-AstraZeneca ce allura ta farko da aka fara amfani da ita a Najeriya kuma bisa bayanan wani rahoton BBC, an sarrafa shi ne da kwayar cutar mura (wadda ake kira adenovirus) wadda aka samu daga biri amma an inganta shi da kwayoyin halittan da ke dauke a coronavirus – sai dai ba zai iya janyo ciwo ba.

Allurar Moderna wanda gwamnatin Najeriya ke amfani da shi yanzu ana iya ajiye shi a fridge mai sanyin digiri 2 zuwa 8 a ma’aunin selshiyus, kuma alluran da ba’a bude ba suna iya zama cikin fridge na tsawon kwanaki 30 a cewar hukumar yaki da cututtuka CDC. Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta shawarci ba da tazarar kwanaki 28 tsakanin alluran biyu. Allurar na da karfin bayar da kariya na kusan kashi 94.1 bisa 100 daga kwanaki 14 bayan karban kashin farko na alluran.

Johnson & Johnson na bukatar sanyi sosai a wurin ajiya. A cewar kamfanin, allurar na iya kaiwa har shekaru biyu idan har aka ajiye ta a dakin sanyi mai digiri -20 (ashirin kasa da sifili) bisa ma’aunin selshiyus sa’annan shi ma zai iya kai wa kwanaki 30 a cikin fridge mai sanyin digiri 2 zuwa 8 a ma’aunin selshiyus.

Da yake bayani kan allurar, babban darektan NPHCDA Dr Faisal Shu’aib ya ce J & J ba ya bukatan wani sanyi na musamman ana iya ajiye shi kamar yadda ake ajiye sauran alluran rigakafi. Haka nan kuma, inda Johnson and Johnson ta fi Moderna da Oxford-AstraZeneca shi ne allura daya ake bukata ba biyu ba kamar sauran. Dan haka ya fi su saukin hulda tunda zai rage wahalar zuwa wurare masu nisa da wahalar shiga.

Dr Shu’aib ya ce za’a yi amfani da kashin farko na alluran J&J a yankunan da ke da wahalar shiga da kuma tsofaffi wadanda ba su da karfi sosai, a duk fadin kasar tun da sau daya kadai ake yi.

Abin da Kwararru a Najeriya ke ce wa

A yayin da ake cigaba da samun karuwar masu fargaba dangane da banbancin alluran rigakafin COVID-19 da ke shigowa kasar, kwararru a Najeriya sun kwantar da hankulan jama’a kan alluran uku, inda suka ce NAFDAC ta amince a yi amfani da dukansu uku har ma ta ce za’a iya amfani da su a kan wadanda suka kamu da cutar a matsayi na gaggawa kamar yadda Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta bayyana.

Hukumar kula da lafiya ta kasa NPHCDA da kungiyar likitocin Najeriya (NMA) sun jaddada cewa Moderna, Johnson & Johnson da Oxford-Astrazeneca duk amintattun allurai ne wadanda ke da karfin yaki da COVID-19.

Babban darektan NPHCDA Faisal Shu’aib yayin da ya ke zantawa da manema labarai a Abuja ya sake tabatarwa ‘yan Najeriya cewa duk wata allurar da NAFDAC ta aimince da ita, na da karfin byar da kariya da kuma yakar cutar.

NPHCDA ta ce duk wadanda suka riga suka karbi kashin farko na allurar AstraZeneca za su karbi na biyun a watan Ogosta sadda raguwar 5000 din da ake sa ran samu za su iso kasar. Da cewa haka, Dr Shu’aib na nufin cewa bisa shawarar WHO bai kamata wanda ya karbi AstraZeneca ya ji ya anshi Moderna da aka kawo yanzu ba, wajibi ne ya karasa da AstraZenecar da ya riga ya fara.

Ita ma kungiyar likitocin Najeriya (NMA) ta sake kwantar da hankulan jama’a dangane da allurar Moderna, inda ta ce lallai allurar na da karfin yakar kwayar cutar COVID-19. Shugaban kungiyar Dr Japhet Olugbodi ya ce “Moderna na da karfin kashi 94 cikin 100 na kare jama daga kamuwa da cutar sa’annan kashi 90 cikin 100 na kumawa da matsanancin nau’in cutar.

Tags: AbujaHausakoronaLabaraiNewsNPHCDAPREMIUM TIMESUNICEF
Previous Post

Hukumar shirya zaɓe ta jihar Kaduna ta dage zaɓuka a ƙananan hukumomi 4 a jihar

Next Post

Labarin da aka saka a Facebook dake cewa an fidda sunayen wadanda suka yi nasarar shiga shirin N-Power gaskiya ne – Binciken DUBAWA

Silas Jonathan

Silas Jonathan

Next Post
Npower

Labarin da aka saka a Facebook dake cewa an fidda sunayen wadanda suka yi nasarar shiga shirin N-Power gaskiya ne - Binciken DUBAWA

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Ramalan Yero ya fice daga PDP, ya ce jam’iyyar ta ishe shi haka nan
  • Ba za mu bari a yi mana rinto da rana tsaka ba, mutanen Kaduna mu suka zaɓa – Ashiru
  • TATTALIN ARZIKI: Gwamnatin Tarayya ta tara naira tiriliyan 10.18 a 2022
  • KURUNKUS: Kwamitin Amintattun jam’iyyar NNPP sun kori Kwankwaso daga Jam’iyyar Kwatakwata
  • Kotu ta ci tarar gwamnatin Kano Naira biliyan 30 saboda rusa ginegine ba bisa ka’ida ba

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.