Gwamnonin Najeriya su 36 sun maka Gwamnantin Shugaba Muhammadu Buhari Kotun Koli, su na zargin Buhari ya karkatar da kuɗaɗen da aka ƙwato daga ɓarayin gwamnati har naira tiriliyan 1.8, sai kuma kadarorin da aka ƙwaro na naira biliyan 450.
Gwamnonin dai sun yi zargin cewa Gwamnatin Buhari ta danƙara kuɗaɗen cikin Asusun Tara Kuɗaɗen Shigar Gwamnatin Tarayya, wato ‘Consolidated Revenue Account’ (CRA), wanda yin hakan kuwa babban laifi ne, kuma take Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ne ƙarara.
Gwamnonin 36 sun shaida wa Kotun Ƙoli cewa, dokar tsarin mulkin Najeriya cewa ta yi a tara kuɗaɗen da kadarorin a ƙarƙashin Asusun Tara Kuɗaɗe pDa Kadarorin Sata Na Gwamnatin Tarayya, wato ‘FGN Assets Recovery Account’ (FGNARA) da ke a Babban Bankin Najeriya.
A cikin kwafen ƙarar da su ka shigar, sun ce abin da gwamnatin Buhari ya yi ya karya dokar ƙasar nan ƙuru-ƙuru.
“Asusun Gwamnantin Tarayya nan ne ya wajaba a tara kuɗaɗen a cikin Asusun Tara Kuɗaɗen Sata, Babban Bankin Najeriya. Saboda shi ne asusun da doka ta yarda a riƙa raba kuɗaɗen da ke ciki tsakanin Tarayya, Jihohi da Ƙananan Hukumomi.
“Shi kuma Asusun Tara Kuɗaɗen Shigar Gwamnatin Tarayya na CRA, asusu ne kawai na tara wa gwamnatin tarayya kuɗaɗen shiga da su ka haɗa da kuɗaɗen harajin da lasisin da gwamnatin tarayya ke karɓa, kuɗaɗen harajin filaye da gonaki, kuɗaɗen ruwa da gwamnatin tarayya ta karɓa daga waɗansu hannayen jarin ta da sauran su.”
Babban Daraktan Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya 36 (NGF), Asishanu Okauru ne ya bayyana haka a cikin kwafen takardar da ya maka Gwamnantin Tarayya ƙara, a madadin ƙungiyar gwamnonin.
“Abin da Gwamnatin Buhari ta yi ya saɓa wa Sashe na 162 (1), 162 (10) da kuma Sashe na 80 na Dokar Kuɗaɗe ta 1958.” Inji Okauru.
Ya ce dukkan waɗannan sassa sun nuna cewa a Asusun Gwamnantin Tarayya za a riƙa ajiye dukkan kuɗaɗen da aka karɓo daga ɓarayin gwamnati, a cikin Asusun Bai Ɗaya Na Gwamnatin Siriya.
Gwamnonin Najeriya 30 Sun Nemi Kotun Ƙoli Ta Tilasta Wa Shugaba Buhari:
1. Ya maida naira tiriliyan 1.8 daga Asusun CRA da kuma Kadarorin naira biliyan 450 duk zuwa cikin Asusun FGNARA da ke cikin Baban Bankin Najeriya, CBN.
2. Sun buƙaci Kotun Ƙoli ta tilasta wa Shugaba Buhari bayyana dalla-dallar adadin kuɗaɗen da aka ƙwato a hannun ɓarayin gwamnati, waɗanda bai saka a Asusun Gwamnantin Tarayya ba.
3. Kotun Ƙoli ta tilasta wa Hukumar Raba Kuɗaɗen Gwamnatin Tarayya (RMFAC), ta tsara yadda za a riƙa raba kuɗaɗen Gwamnanti tsakanin Tarayya da Jihohi da Kananan Hukumomi.
Babban Lauya kuma fitaccen nan Femi Falana ke jagorantar lauyoyin Gwamnonin Jihohi su 36.
PREMIUM TIMES ta samu kwafen ƙarar wadda aka shigar tun a ranar 16 Ga Yuni, 2021. Yayin da Ministan Shari’a Abubakar Malami wanda shi aka shigar ƙarar, ya ke kare gwamnatin tarayya, a ƙarar mai lamba SCN/CV/393/2021.
Yadda Gwamnonin Najeriya 36 Su Ka Gano Buhari Ya Karya Dokar Ƙin Ajiye Kuɗaɗen:
Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya, Kayode Fayemi ya jagoranci gungun wasu ƙwararrun lauyoyi, tare da goyon bayan dukkan Gwamnonin Najeriya su 36. Sun gano cewa an karkatar da kuɗaɗen a Asusun CRA, maimakon a ajiye su a FGNARA.
Sun nuna damuwar su dangane yadda Buhari, mutumin da ke yawan cewa yaƙi da cin hanci da rashawa, amma kuma ya ke tauye wa jihohi haƙƙin da dokar kuɗaɗe ta bai wa jihohin.
Sannan kuma sun nuna Buhari na ƙin bin sharuɗɗa, dokoki da ƙa’idojin da Gwamnatin Tarayya ta shimfiɗa wajen yi wa Asusun FGNARA da Asusun CRA karan-tsaye.
Sun bayyana wa Kotun Ƙoli cewa kuɗaɗen da su ke so Buhari ya maida a Asusun Gwamnantin Tarayya na Bai Ɗaya Da Jihohi, sun tashi naira tiriliyan 1, 836, 906, 543, 658.78.
Kuɗaɗen dai an ƙwato su a hannun ɓarayin gwamnati da sauran masu laifi daban-daban daga 2015.
Sannan kuma su na neman kason jihohin su a cikin kadarorin naira biliyan 450 da aka ƙwato tun daga 2015.