Ministan Ƙwadago Chris Ngige ya yi gargaɗin cewa aikin likita a Najeriya ya shiga garari da gararamba, ganin yadda likitocin ƙasar nan su ka maida yajin aiki kamar wani abin tinƙaho a rayuwar su.
Ngige ya yi kira ga likitoci su daina ɗagawa da girman kai, saboda su na ganin kamar su ne ke ceton rayukan mutane.
Minista Ngige na magana ne a kan yajin aikin da Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa (NARD) ke yi tun a ranar 2 Ga Agusta.
Ya yi wannan bayani ne a Taron Ƙungiyar Dattawan Likitoci, wanda aka yi a Abuja.
A taron an tattauna Matsayin Aikin Likita a Jiya da Yau da kuma Gobe.
“Ba a taɓa samun lokacin da aikin likitanci ya shiga mummunan hatsari a ƙasar nan kamar a halin da mu ke ciki a yanzu ba. Daga inda na ke tsaye a nan ko zaune, ina hango gagarimar matsala a wannan fanni ta tunkaro ƙasar nan.
“Likitoci ba su tashi yajin aiki sai lokacin da likita ɗan uwan su ke kan muƙami. Minista Onyebuchi Chukwu da Minista Adebowale duk sun sha fama da yajin aiki a baya.
“Ga shi daga hawa na tsawon shekaru shida kenan, amma an yi min yajin aiki sau huɗu. Wasun mu kuma duk mun yi waɗannan ƙungiyoyi, musamman NARD.”
Da ya ke magana, Shugaban Ƙungiyar Likitoci Gaba Ɗaya ta Najeriya (NMA), Innocent Ujah, ya bayyana halin ƙuncin da likitocin Najeriya ke ciki, kuma su ke ci gaba da fuskanta daga manyan su har ƙanana.
Ya koka dangane da yadda Hukumar Tsara Albashin Ma’aikata (NSIWC) ta fitar da sanarwar za a daina biyan likitocin da ke koyarwa a jami’a alawus ɗin CONMESS.
Sannan ya yi ƙorafin yadda duk ilimin ka in dai kai likitanci ka ke koyarwa, to ba za a zaɓe ka shugabancin Jami’ar Jihar Legas ba.
Ujah ya ce haka kawai ana jin haushi da ganin ƙyashin likitoci, ba tare da yin la’akari da irin shekarun da su ke shafewa wajen neman ilimi ba, da kuma irin hatsarin da su ke shiga wajen gudanar da aikin su.
Ƙungiyar Likitocin NARD ta tsunduma yajin aiki, saboda gwamnati ta ƙi cika masu alƙawarran biyan su haƙƙoƙin su da ta ɗauka a rubuce tsawon watanni fiye da uku da su ka gabata.
Farkon makon nan PREMIUM TIMES HAUSA ta buga labarin yadda gwamnati da ƙungiyar likitoci su ka shiga rikici, yayin da su ka bar marasa lafiya ‘mutu kwakwai rai kwakwai’
Kalamai marasa dadin ji da Gwamnatin Tarayya da Ƙungiyar Likitoci ta NARD ke antaya wa juna, yanzu dai talakawa da marasa galihu da ba su iya zuwa asibitin kuɗi lamarin ke addaba.
Yayin da likitocin su ka ce ba za su koma aiki ba, har sai Gwamnantin Tarayya ta biya su haƙƙoƙin su domin su samu damar ɗaukar ɗawainiyar riƙe iyalan su, ita kuma Gwamnantin Tarayya ta ce duk likitan da bai koma bakin aiki ba, to ya fitar da rai daga karɓar albashin sa.
Na Ce Kada A Biya Likitoci Albashi Sai Sun Koma Bakin Aiki -Minista Ngige:
A wata tattaunawa da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels, Ministan Ƙwadago Chris Ngige ya furta cewa ya bada umarnin kada a biya duk wani likita da ke aiki a ƙarƙashin gwamnanti albashin sa, in dai ya tafi yajin aiki, har sai ranar da ya koma za a fara lissafi.
“Likitocin nan fa sun raina Najeriya. Na kuma bada umarnin idan su ka ƙara kwana bakwai ba su koma ba, to duk za a kore su.”
Wannan wa’adin dai zai ƙare ne a ranar Litinin mai zuwa ta gobe.
Minista Ngige Karan-kaɗa-miya, Mun Fi Ƙarfin Tsayawa Faɗa Da Shi -Likitocin NARD:
Shugaban Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa (NARD), Okhuaihesuyi Uyilawa, ya bayyana wa Minista Ngige cewa shi fa ba kowa ba ne sai ministan ƙwadago.
Ya ce Ngige ya daina cika baki da hura hanci, tunda ba shi ne Shugaba Muhammadu Buhari ba.
Batun janye yajin aiki kuwa, Uyilawa ya ce ba za su koma ba. “Sai dai a fara biyan mu haƙƙin mu tukunna kafin mu koma. Tunda dai mun lura wannan gwamnati ba mai cika alkawarin yarjejeniyar da mu ke ƙullawa ba ce.
“Sannan mu fa mun fi ƙarfin a yi mana barazana da kora. Idan ya sa an kore mu sai me, tunda ba biyan mu haƙƙin mu ake yi ba? Kuma ba shi ne farkon fara korar likitoci ba. Tsakanin 2010 da 2014 Ministan Lafiya na lokacin Onyebuchi Chukwu ya kori likitoci daga aiki. Saboda haka idan yanzu Ngige ya kore mu, ba kan sa farau ba. Wancan lokacin da aka kori likitoci ai asibitocin ƙasar nan kusan durƙushewa su ka yi.
“Yanzu ma idan Ngige ya kore mu, ya zama Ministan da ya kori likitoci don sun nemi a biya su haƙƙin su.”
A makon jiya dai PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin yadda Buhari da likitocin Najeriya su ka ƙaurace wa asibitocin ƙasar nan lokaci guda.
Kamar jira su ke yi Shugaba Buhari ya tafi Landan ganin likita, su kuma Ƙungiyar Likitoci ta NARD sai su ka tsunduma yajin aikin da su ƙaurace wa asibitocin ƙasar nan, ko allura su ka daina yi wa majiyyata.
A makon da ya gabata dai Shugaba Buhari ya yi kwanaki fiye da 200, jimlace a Landan da sunan zuwa ganin likita, a tsawon shekaru shida da ya shafe a kan mulki.
Asibitocin ƙasar nan da dama sun wayi garin Litinin da yajin aikin likitocin da ke ƙarƙashin ƙungiyar NARD. Wakilan PREMIUM TIMES sun zagaya asibitoci a garuruwa daban-daban, kuma sun tabbatar da haka.
A Asibitin Gwamnantin Tarayya na Legas da ke Ebute-Metta, wakilin mu ya samu likita ɗaya tal ya ganin marasa lafiya sama da 300, a ranar Litinin ɗin da aka fara yajin aikin.
Wani da ya zanta da shi, ya ce ya kai matar sa asibitin ne, kuma ita ce ta 45 a layi. “Amma kuma har zuwa yanzu ƙarfe 3 na yamma ba a zo kan ta ba. Wasu ma duk sun koma gida a fusace, kuma cikin damuwa.” Inji Inanaco.
A Abuja kuwa, wakilin mu ya leƙa Babban Asibitin Ƙasa, wanda Najeriya ke ji da shi, kuma na fita-kunya.
Wani mai suna Lucky Oche da ke jiyyar mahaifin sa, ya shaida wa wakilin mu cewa marasa lafiya a asibitin hankulan su a tashe ya ke. “Saboda kowa tsoro ya ke ji idan yajin aikin ya daɗe, za a sallami da wanda ya ji sauƙi da wanda bai ji ba, duk a sallame su baki ɗaya.”
Kusan haka lamarin ya ke s yawancin asibitocin ƙasar nan tun daga ranar Litinin, kuma alamomi na nuna cewa lamarin ya na ci gaba da dagulewa.
Likitocin dai sun tafi yajin aiki ne saboda gwamnatin tarayya ta ƙi cika masu alƙawarin da ta ɗauka t CTun cikin watan Afrilu, bayan sun shafe watanni a baya su na gargajiya kafin a kai ga ɗaukar alƙawarin.
Discussion about this post