• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Tsokaci game da maganar tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Babangida, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
August 8, 2021
in Ra'ayi
0
Ibrahim Babangida

Ibrahim Babangida

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

Assalamu Alaikum

Ya ku ‘yan uwana ‘yan Najeriya, masu girma, masu daraja, masu albarka! Kamar yadda kuka sani, dukkanin mu dai muna ji, muna sane, kuma muna ganin irin halin da kasar nan tamu mai albarka ta samu kan ta ciki a yau? Wanda abu ne a fili karara, wanda ba ya bukatar sai an yi ta lissafo matsalolin kasar nan a koda yaushe, sam ina ganin babu bukatar yin hakan, kawai dai abun sani shine, KOWA YA YARDA, KUMA KOWA YA AMINCE CEWA, AKWAI MATSALA A KASAR NAN!

Don haka, abun da kawai zamu ci gaba da yi a halin yanzu shine, kokari, da bayar da gudummawar samar da mafita daga wadannan matsalolin, tare da bin halastaccin hanyoyi, kuma ingantattu, domin samar da mafita, tare kuma da hada wa da yin addu’a da rokon Allah ya kawo muna mafita mai dorewa!

‘Yan uwana masu girma! Zan gaya maku gaskiya, kuma tsakanina da Allah, ba tare da la’akari da wani, ko wasu ba. Kuma zan fadi wannan magana ne, ba tare da wata shakka ko jin tsoron wani ba, kuma ba tare da wata manufa ta cin mutuncin wani ko wasu ba, ko tozarta wani ko wasu ba. Kuma wannan magana da zan fadi, zan fade ta ne, tare da sani na da kuma imanin cewa zan hadu da Allah, zan tsaya gaban Allah, gobe alkiyama, domin in amsa tambayoyi a kan ta. Don haka, wannan magana, bani da wani shakku ko kokwanto a kan ta.

Sannan wannan magana tawa, idan na fade ta, ina sane da cewa, lallai mutane zasu fahimce ta, tare da kokarin fassara ta a iya matsayin fahimtarsu, ko ra’ayinsu, da kuma tunaninsu. Don haka, ba zan taba damuwa da yadda kowa ya fahimce ta ba, ko ya fassara ta. Kawai manufata akan wannan rubutu, wallahi shine kishin kasa ta Najeriya, da kuma kishin al’ummata, da kuma neman yardar Allah mahaliccina kawai, wannan shine!

Ya ku bayin Allah, al’ummar Najeriya! Kamar yadda kuka sani, tsohon shugaban kasar Najeriya, mai girma Janar Ibrahim Badamasi Babangida (Allah yasa ya gama lafiya, amin), yayi hira da wata fitacciyar jarida a kasar nan, ko gidan talabijin na turanci, mai suna ‘Arise TV’, a inda ya kawo wasu muhimman maganganu da shawarwari masu muhimmanci, masu kyau, wadanda suke cike da ilimi, da hangen nesa; magana ta dattako, wadda lallai idan ‘yan Najeriya suka rike ta, kuma suka yi aiki da ita tsakaninsu da Allah, ba tare da la’akari da wani ra’ayi ba, to ina mai tabbatar maku da cewa, wallahi, Allah Subhanahu wa Ta’ala, zai taimake mu, ya tausaya muna, yasa muna hannu cikin lamurran mu, kasar mu Najeriya ta gyaru, a zauna lafiya, da ikon Allah!

Janar Ibrahim Babangida dai ba jahili ba ne, mutum ne shi mai ilimi da hangen nesa. Shi mutum ne mai cikakken kishin kasar nan da kuma al’ummarta. Shi mutum ne da ya sadaukar da rayuwarsa, domin ci gaban kasar nan da hadewarta wuri guda, da kuma zaman lafiyarta. Yasan ciki da wajen kasar nan. Allah ya fahimtar da shi matsalolin kasar nan. Mutum ne da baka isa ka zage shi, ko ka soke shi ba, sai dai idan kai mahassadi ne, ko kuma wanda baya son ci gaba, wannan kuma babu abunda zamu ce da kai, illa ka je kayi ta hassadarka, kuma Allah ya fi ka!

Kuma ni, ba wai ina nufin Janar Ibrahim Babangida baya da kuskure ko kasawa ba, a’a, ba haka ba ne. Shi mutum ne, dan Adam, kamar kowa, kuma shi ajizi ne; zai iya yin daidai, kuma zai iya yin kuskure a cikin dukkanin lamurransa. Amma dai, duniya tayi shaida akan wannan bawan Allah, cewa daidai din sa da alkhairansa, sun fi kusakurensa yawa. To tun da haka ne, me ya kamata muyi? Sai mu roki Allah ya yafe kusakurensa, daidai din sa kuwa Allah ya biya shi da mafificin sakamako, duniya da lahira.

Ya ku Jama’ah! Janar Ibrahim Babangida yace bai kamata duk mutumin da zai shugabanci kasar nan ba ya kasa wasu siffofi da halaye da dabi’u masu muhimmanci, kuma nagari. Daga cikin wadannan halaye da dabi’u da siffofi na gari, yace duk mutumin da tsufa ya mamaye shi, bashi da karfin da zai jagoranci al’ummah, wato mai yawan shekaru, kuma mutumin da ya haura ko ya wuce shekaru sittin (60) a duniya, to bai dace ya zama shugaban kasar nan ba. Domin irin wannan mutum, babu wani abu da zai iya kullawa kasar nan in ban da shiririta da tanbele da shirme da rashin tabbas.

Wannan ra’ayi na Janar Ibrahim Babangida ai ko addini ma ya tabbatar da shi. Domin ba’a bayar da shugabanci ga mutum mai rauni, ko marar lafiya da sauransu!

Ya ku ‘yan uwana ‘yan Najeriya! Wallahi, wallahi, wallahi, babu wanda zai soki Janar Ibrahim Babangida akan wannan magana sai wanda yake wawa, jahili, dakiki, wanda sam bai san me yake yi ba.

Ku sanai, Najeriya kasa ce muhimmiya a gare mu. Bamu da wata kasa da muke so, kuma muke kauna, kamar Najeriya. Bamu da wani wuri, wurin zuwa, kamar Najeriya. Don haka, wallahi, ba zamu taba yin shiru, akan duk wani mutumin da yake so ya cuci kasar nan ba, ko a hada kai da shi, a zalunci kasar mu mai albarka, wato Najeriya. Wannan mutum ko dan kudu ne shi, ko dan arewa ne. Ko musulmi ne ko kirista ko marar addini. Kuma ko wane yare ne shi, ko kabila; wallahi duk wannan bai dame mu ba. Abun da ya dame mu kawai, KASAR MU NAJERIYA, DA MAKOMARTA, DA AL’UMMARTA!

Jama’ah, duk wani mutum da yasan abun da yake yi, kuma yasan meye mulki da shugabanci, to yasan cewa duk mutumin da yake tsoho marar karfi, ko marar lafiya, ya kamata ya hakura, ya huta; su zama iyaye, su zama masu bayar da shawara idan suka ga na kasa da su na neman kaucewa daga hanya, kuma su kame kan su daga neman shugabancin kasar nan!

Ya ku ‘yan uwana ‘yan Najeriya, wallahi ya zama dole, kuma wajibi akan duk wani dan Najeriya, mai kishin kasar nan da gaske, kuma tsakaninsa da Allah, musa ido sosai, akan duk wasu mutane, ‘yan cuwa-cuwa, masu kishin aljihunsu, ‘yan 419, wadanda suke kokarin cusa muna ra’ayin cewa dole sai mun goyi bayan wani mutum; kuma duk da cewa, dalilai na ilimi da na hankali, duk sun tabbatar muna da cewa wannan mutum ba ya da cikakkiyar lafiya ko karfin da zai shugabanci kasar nan, sannan kuma ga yawan shekaru! Wadannan mutane ba Allah ne a gabansu ba, ba kasar nan ce a gabansu ba, ba al’ummah ce a gabansu ba! Kawai su matsalarsu, shine me zasu samu kawai. To ya zama dole mu sa ido matuka, akan irin wadannan miyagun mutane, bata-gari, ‘yan jari-hujjah; ‘yan fashin ‘yancin al’ummah, da jin dadinsu, da walwalarsu!

Kuma wallahi, ina mai sake tabbatar maku da cewa, goyon bayan Janar Ibrahim Babangida akan wadannan maganganu da yayi, wajibi ne, dole ne, kuma tilas ne! Sannan duk wani mutum, ko shi waye, kuma ko wace jam’iyyah yake, ko shi dan kudu ne ko dan arewa, musulmi ne ko kirista ne, idan kuka ji yana sukar maganganun wannan bawan Allah, to shi munafuki ne, dan cuwa-cuwa, kuma marar kishin kasar nan ne!

Don haka, mu sani, a halin yanzu, irin halin da wannan kasar take ciki, irin wadannan halaye munana da Allah ya jarabi kasar nan da su, to tabbas, tana bukatar irin mutumin da Janar Ibrahim Babangida ya bayyana muna a cikin jawabansa, da kuma hirarsa mai albarka!

‘Yan uwa na ‘yan Najeriya, wallahi, kar ku sake yarda a sake yaudarar ku da maganar bangare ko jam’iyyah ko addini ko yare; duk wannan yaudara ce, kuma ha’inci ne. Najeriya a halin yanzu tana bukatar jajirtaccen shugaba, mai lafiya, mai karfi a jiki, mai sauraron shawarwarin a’ummah, mai cikakken kishin kasa, mai imani, mai tausayi, mai tsoron Allah, masanin tattalin arziki, wanda kuma ya fahimci kasar nan da matsalolinta, fitacce, wanda kuma aka sani a fadin kasashen duniya!

Kar mu yadda da rudin duk wani munafuki, mai kishin aljihunsa, ba kasarsa da a’ummarta ba!

Kuma mu sani, wallahi duk wanda ya goyi bayan wani mutum daga cikin ‘yan siyasa; kuma yana sane da cewa wannan mutum marar lafiya ne, mai rauni ne, wanda bai da karfin da zai jagoranci kasar nan, to ya sani cewa, YA CUCI AL’UMMAR NAJERIYA, YA YAUDARESU, YACI AMANARSU KUMA YA HA’INCESU, kuma ya san cewa, zai tsaya a gaban Allah gobe alkiyama, domin amsa tambayoyi, akan wannan goyon baya da ya ba wannan mutum mai rauni. Don haka sai mu sake tunani. Kuma yanzu ya rage na mu! Mu sani, kamar yadda akwai rayuwa, to kuma tabbas akwai mutuwa, kuma akwai tsayuwa a gaban Allah, kuma tabbas akwai hisabi!

Daga karshe, ya ku ‘yan siyasar Najeriya! Ku sani, ko wace jam’iyyah kuke ciki, wallahi, al’ummar kasar nan suna bin ku babban bashin tsayar masu da mutum mai lafiya, mai cikakken karfin da zai jagoranci kasar nan, kuma mai cikakken kishin kasar nan; mai imani da tausayi da tsoron Allah, wanda mulkinsa zai zama alkhairi ga kasar nan baki daya, kuma kowa ya amfana da karfin ikon Allah. Amma idan kuka ki jin wannan shawara, kuka bi son zuciyar ku, kuka fifita son abun duniya akan maslahar kasarku, to ku sani, duk zamu mutu, mu tsaya a gaban Allah, da mu da ku, domin amsa tambayoyi a gabansa! Kuma kafin nan, sai kun yi dana-sanin aikin da kuka yi, wallahi tun anan duniya!

Wassalamu alaikum,

Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad Gusau, Babban limamin Masallacin Juma’ah na Nagazi-Uvete, ya rubuta daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samunsa a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaBabangidaHausaIbrahimIbrahim BabangidaLabaraiNajeriya
Previous Post

Ƙasashen Afrika ta Yamma za su yi amfani da tsarin sa ido a zaɓe na INEC — Farfesa Yakubu

Next Post

Shin da gaske ne Kano na shirin saka dokar hana mata tukin mota? Binciken DUBAWA

Next Post
Ganduje ya naɗa Shugaban Riƙon Hukumar Hana Cin Hanci ta Kano, bayan dakatar da Muhyi Magaji

Shin da gaske ne Kano na shirin saka dokar hana mata tukin mota? Binciken DUBAWA

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • KATSINA BA DAƊI: Mahara sun buɗe wa tawagar Buhari wuta a yankin da su ka bingige Kwamandan ‘Yan Sandan Dutsinma
  • Takardun sakandare na sun yi layar-zana, amma ina da sakamako mafi kyau -Okowa, mataimakin takarar Atiku
  • HAJJIN BANA: Hankulan maniyyatan Kano 1,238 ya tashi saboda kasa kwashe su kan lokacin rufe filin jirgi Jeddah
  • IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi
  • 2023: Ka zaɓi El-Rufai mataimaki, ‘ka yi nasara a zaɓe kamar yankan wuka’ – Kira ga Tinubu

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.