• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Shin da gaske ne Kano na shirin saka dokar hana mata tukin mota? Binciken DUBAWA

Silas JonathanbySilas Jonathan
August 8, 2021
in Labarai
0
Ganduje ya naɗa Shugaban Riƙon Hukumar Hana Cin Hanci ta Kano, bayan dakatar da Muhyi Magaji

Zargi: Wani sakon da ake yadawa a kafofin sadarwar internet na rade-radin wai jihar Kano na shirin hana mata tuka motocinsu a jihar.

Jihar Kano da wasu jihohi 11 da ke yankin arewacin Najeriya na amfani da tsarin dokar shari’ar musulunci wanda aka aka kafa tun a shekarar 2000.

Wannan dokar ta haramta shan giya, zina, luwadi da ma zance tsakanin na miji da na mace a cikin bainar jama’a domin hakan alama ce ta fitsari ko rashin tarbiya. Duk wanda aka kama zai fuskanci hukuncin kamar yadda shari’ar musulunci ta gindaya.

A Kwananakin nan kafofin yada labarai sun sake samun labari makamancin wannan, wanda ke zargin gwamnatin Kanon da aiki kan wata doka cikin sirri, inda ake zargi dokar za ta hana mata tuka motoci a jihar Kano.

Labarin wanda aka fara wallafawa a shafin The Reflector na zargin cewa shawarar wani shirin boye ne tsakanin gwamnati da majalisar Ulaman jihar.

“Bayan sun dakile ko wace kafa ta samun wani mataki na bazata dangane da abin da suke yi, gwamantin jihar Kano tare da majalisar ulamanta na shirin zartar da dokar ta za ta haramtawa mata tuka mota a jihar. Dokar za ta shafi mata har da wadanda ba musulmi ba,” a cewar labarin.

“Hakan ya biyo bayan taron sirrin da aka yi a ma’akatar shari’a lokacin hutun sallah tsakanin Kwamishanan kula da harkokin addinai Dr Mohammed Tahir (Baba Impossible) da kungiyar malamai/ulama a karkashin jagorancin Sheikh Abdulwahab Abdallah BUK”

Rahoton ya kuma kara da cewa ana aiki a kan kudurin wannan dokar a ma’aikatar shari’a kuma nan ba da dadewa ba za’a gabatar da shi a gaban Majalisar dokokin jiha domin ta amince da shi ta zamar da shi doka.

Wannan kira na haramtawa mata tuki na karkashin jagorancin Sheikh Abdallah Usman Umar Gadon Kaya wanda ya ce kyale mata su na tuki a jihar na zaman lokaci mai duhu ga musulmi. Labarin ya kuma cigaba da cewa: A gudunmawarsa Dr Sani Umar Rijiyar Lemo ya ce kamata ya yi a ce Kano ta yi koyi da Saudiyya wadda a cewarsa, al’umma ce da ke aiki da dokokin shari’a. Shi kuma a nasa ra’ayin Sheikh Abdallah Pakistan cewa ya yi yanzu ne ya kamata a zartar da wannan doka, babu lokacin da ya fi wannan ganin cewa jihar na fiskantar wani yanayi na fadakarwar musulunci a karkashin Ganduje.

“Daga farkon taron, kwamishanan kula da harkokin addini, Baba Impossible ya tabbatarwa mahalarta taron cewa gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bayar da kai wajen wanke Kano daga duk munanan halaye na zamantakewa.

“A matsayin mabiyi addinin musulunci gwamna Ganduje zai yi duk abin da zai iya wajen sanya kano bisa turbar gaskiya da irin tarbiyar da ke girke a addinin Islam,” ya ce.

Mahalarta taron sirrin a cewar rahoton sun hada da “Sheikh Abdallah Usman Umar Gadon Kaya, Sheikh Abdallah Pakistan, Sheikh Abdulwahab Abdallah BUK, Sheikh Sani Umar Rijiyar Lemo, Farfesa Salisu Shehu, Dr Aliyu Umar Al-Furqaan da wasu wadanda ba’a fayyace ba.

Idan har kudurin ya zama doka, dokar za ta haramtawa mata tuki a jihar ko da kuwa matan ba mabiya addinin musulunci ba ne.

Mutane fiye da 5,000 sun ga wannan labarin. Bayan haka, an raba shi a soshiyal mediya inda wasu karin jama’a suka yi ma’amala da shi.

Tantancewa

Dubawa ta fara da neman mahimman kalmomi inda ta gano cewa ban da shafin The Refelections babu wata sahihiyar kafar yada labaran da ta yi amfani da labarin a kasar baki daya. Sa’annan kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Mohammed Garba ya karyata wannan zargin a wata sanarwar da ya fitar ranar talata, Malam Garba ya kwatanta rahoton a matsayin karyar ba ta da tushe.

Wanann labarin ba shi da sahihanci shi ya sa ba’a iya tantance majiyoyin labarin,” ya ce.

Malam Garba ya ce gwamnatin jihar ba zata gudanar da wani “taron sirri” domin ta yanke shawara kan batun da ya shafi dimbin jama’ar jihar ba, ya kuma kara da cewa ko ita kanta Saudiyya wadda jagora ce a addinin musulunci, ta cire dokar da ta hana mata tuki a kasar a 2018.

Rahoton ya ambato daya daga cikin malaman addinin da suka kasance a taron na cewa ya dace Kano ta yi koyi da Saudiyya tunda “al’umma ce mai amfani da dokokin sharia.”

Sai dai bincike ya nuna cewa mata sun yi shekaru uku suna tuki yanzu a Saudiyya.

A 2018, gwamnatin Saudiyya ta cire dokar da ta hana mata tuki. Yerima mai jiran gado Mohammed bin Salman wanda aka fi sani da inkiyarsa MBS ne ya jagoranci hambarar da dokar a matsayin daya daga cikin matakan habaka tattalin arzikin kasar ta yadda ba za ta rika dogaro da man fetur kadai ba.

Wannan mataki ya nemi ya bude al’ummar Saudiyya ga sauran kasashen duniya domin ta janyo masu zuba jari. Shugabanin kasar sun yabawa yeriman kuma sauran kasashen duniya na mi shi kallon mai rajin kare hakkin mata.

Ko da shi ke, haramta mata tukin da aka yi a Saudiyya, abu ne da ya shafi al’ada ba kamar yadda dokokin da aka sanya a yankin arewacin Najeriya suka shafi addini ba.

Kwamishinan ya kuma nuna farincikinsa da cewa yawancin malaman da aka ambato a rahoton sun riga sun nisanta kansu daga labarin.

Daya daga cikinsu Sheikh Abdullah Kaya ya ce labarin karya ne wato “Fake News”

“Ni Abdullah Usman Umar Gadon Kaya, na fada da kakkausar murya wannan labari fake news ne. Bani da hannu a ciki. Wannan harka ce ta makiya, wadanda suke so su tayar da zaune tsaya a jihar Kano da Najeriya baki daya,” malamin ya rubuta a shafin shin a Facebook.

Dubawa ta kuma tuntubi shugaban kungiyar kiristocin Najeriya wato CAN a jihar Kano, reverend Samuel Adeoulu Adeyemo da Sheikh Ibrahim Khali shugaban kungiyar malamai/Ulamas. Su biyun sun ce labarin ba shi da tusheballantana asali.

A karshe

Batun cewa gwamnatin jihar Kano na shirin saka dokar haramtawa mata tuka mota a jihar karya ne. Babu wata sahihiyar kafar yada labarai da ta buga irin wannan labarin a kasar.

Tags: AbujaKanoNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Tsokaci game da maganar tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Babangida, Daga Imam Murtadha Gusau

Next Post

Wasu labarai a shafukan yanar gizo na amfani da hotunan da aka dauka a 2019 a matsayin hotunan yadda aka kai Abba Kyari Amurka – Binciken DUBAWA

Silas Jonathan

Silas Jonathan

Next Post
Abba Kyari ya ja na shi Dalolin daga wurina – In ji ‘Hushpuppi’ a kotun Amurka

Wasu labarai a shafukan yanar gizo na amfani da hotunan da aka dauka a 2019 a matsayin hotunan yadda aka kai Abba Kyari Amurka - Binciken DUBAWA

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Tinubu da INEC sun ƙi amincewa da tulin kwafe takardun da Atiku ya kwafo daga iReV
  • GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya
  • HAJJI 2023: Gwamnatin Filato ta bar mahajjatan jihar su na hajijiya a Madina
  • Kada ku tausaya min don na faɗi zaɓen Sanatan Zamfara – Sanata Marafa
  • JIRAN TSAMMANI: Tinubu zai saka wa waɗanda su ka yi wa APC hidima da waɗanda su ka wahala saboda jam’iyya – Marafa

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.