• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

RAHOTON MUSAMMAN: Yadda Buhari ya yi fatali da shawarar Gwamnoni 36, ya amince a biya naira biliyan 159 da su ka ce gidoga ce ba bashi ba

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
August 31, 2021
in Babban Labari, Rahotanni
0
RAHOTON MUSAMMAN: Yadda Buhari ya yi fatali da shawarar Gwamnoni 36, ya amince a biya naira biliyan 159 da su ka ce gidoga ce ba bashi ba

Shugaba Muhammadu Buhari ya sa hannun amincewa a biya wani bashin da aka yi iƙirarin ana bin jihohi 36 da ƙananan hukumomi 774.

Adadin bashin ya kai dala miliyan 418, kwatankwacin naira biliyan 159 da ya amince a biya wasu mutum shida, duk kuwa da cewa Gwamnonin Najeriya sun daɗe su na nuna wa Buhari cewa babu tabbaci ko wata ƙwaƙƙwarar shaida ko hujjar an yi ayyukan a jihohi har na waɗannan adadin maƙudan kuɗaɗe.

A ranar Talata PREMIUM TIMES ta ci karo da wani umarni da Ma’aikatar Harkokin Kuɗaɗe ta bai wa Ofishin Kula da Basussuka (DMO), cewa ya fara bayar da takardar alƙawarin biyan kuɗaɗe ga waɗanda su ka yi iƙirarin cewa su na bin jihohin da ƙananan hukumomi waɗannan kuɗaɗen.

Hakan dai ya na nufin Shugaba Muhammadu Buhari ya rattaba amincewa a biya bashin kenan.

Wannan mataki da Buhari ya ɗauka ya saɓa da shawarar da Gwamnonin Najeriya su ka sha bayarwa cewa a fara gudanar da ƙwaƙƙwaran bincike a ƙananan hukumomi 774 na ƙasar nan, domin a tabbatar da sahihancin ayyukan da masu iƙirarin bin bashin su ka ce sun yi, amma ba a biya su ba.

Sai dai kuma duk da wannan damuwa da gwamnonin su ka nuna, Buhari ya amince a biya kuɗaɗen tare da yin fatali da shawarar ta su.

Za a biya su kuɗaɗen a tsawon shekaru 10, wato daga nan zuwa 2031. Za a riƙa cira daga cikin kuɗaɗen da Gwamnatin Tarayya ke bai wa Jihohi da Ƙananan Hukumomi duk bayan wata ɗaya.

Wasiƙar umarnin da aka ba Ofishin DMO dai an rubuta ta ne a ranar 12 Ga Agusta, 2021. Dama kuma tun a ranar 11 Ga Janairu Buhari ya amince a fara biyan kuɗaɗen, amma wata tankiya da gwamnoni ta sa ya dakatar.

Waɗanda za a biya kuɗaɗen dai su shida sun haɗa da tsohon Ɗan Majalisar Tarayya Ned Nwoko, wanda ya ke kafa hujja da umarnin biyan wanda Babbar Kotun Tarayya ta Abuja ta bayar a ƙarar da su ka shigar mai lamba FHC/ABJ/CS/148/2017.

Nwodo na neman a biya shi dala miliyan 142,028,941.

Sai kuma wasu mutum uku da ke neman a biya su dala miliyan 143,463,577.76 a ƙarar da su ka shigar mai lamba FHC/CV/2129/2014.

Su ukun sun haɗa da Riok Nigeria Ltd, Orji Nwafor Orizu da wani mai suna Olaitan Bello.

Wanda ya fi saura kason kuɗaɗe a cikin su shi ne Iseghoghi Edwards, mai dala miliyan 159. A bisa hukuncin da Babbar Kotun Tarayya ta Abuja ta zartas mai lamba FCT/CV/1545/2015.

Akwai kuma kamfanin wani mai suna George Uboh, wanda zai karɓi dala miliyan 47,831,920.

Salsalar Zargin Gidogar Da Gwamnonin Najeriya Su Ka Ce An Tafka A Batun Biyan Bashin:

Gwamnonin sun nuna damuwa kan yadda Minista Malami ya ƙi jin gargaɗin zargin harƙalla, ya riƙa ƙoƙarin a biya bashin naira biliyan 159.

An shafe shekaru ba ɗaya ba, ba biyu ba, Ministan Shari’a Abubakar Malami na bijire wa gargaɗin da ake yi masa cewa wasu kuɗaɗe da ya ke ta ƙoƙarin ganin an biya daga cikin kason kuɗaɗen Jihohi da Ƙananan Muhumomi har dala milyan 418 (naira biliyan 159), akwai gidoga a cikin lamarin.

Kuɗaɗen dai an ce wai bashi ne wasu ‘yan kwangila da jami’an tuntuɓa ke bin jihohi da ƙananan hukumomi.

Amma duk da gargaɗin da aka rika yi wa Malami, ciki kuwa har da rahoton da EFCC ta damƙa masa, wanda ta nuna cewa bashin haramtacce ne, ba gaskiya ba ne, shi kuma Minista Malami ya rufe ido sai matsa lamba ya ke yi domin ganin an biya waɗanda aka ce wai su na bin bashin, ta hanyar riƙa cirar kudade ana biyan bashin daga kuɗaɗen da Gwmnatin Tarayya ke bai wa Johohi da Ƙananan Hukumomi a duk ƙarshen wata.

Wannan jarida ta mallaki kwafe-kwafe na takardun da su ka riƙa karakaina da ke nuna yadda Malami ya rufe ido ya ke ta sharce gumin ganin lallai a biya kuɗaɗen, duk kuwa da cewa hatta Ƙungiyar Gwamnoni ta Najeriya, NGF ta bayyana masa cewa binciken ƙwaƙwaf ne kadai zai iya tabbatar da sahihancin bashin ko bogi da gidoganci ne kawai.

‘Yan Ƙaƙuduba Uku:

Sauran mutane biyun da su ka haɗa kai da Minista Malami domin ganin an biya kuɗaɗen ido-rufe, sun haɗa da Shugaban Ma’aikata na Fadar Shugaban Kasa, Ibrahim Gambari da kuma Ministar Harkokin Kuɗaɗe, Zainab Ahmed.

Gungun Wasu ’Yan Gidoga:

Wato akwai wasu ’yan dillancin gidoga da ke iƙirarin su ne wakilan masu bin bashin, waɗanda wakilan mu su ka ji cewa sun yi ƙoƙarin su bai wa Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya, Kayode Fayemi toshiyar bakin dala milyan 40, domin ya haƙura, ya daina tirjiya, ya amince a biya bashin kawai.

Amma Gwamna Fayemi dtin na Jihar Ekiti bai amince ba, ya ƙi karɓar tayin da su ka yi masa, inda ya tsaya kai da fata cewa lallai sai dai a yi ƙwaƙƙwaran binciken ƙwaƙwaf domin a gano gaskyar lamarin.

Sai dai kuma bayan da PREMIUM TIMES ta fallasa wannan ƙaƙudubar, an riƙa ɗaukar nauyin buga wasu bayanan ɓata suna ga Gwamna Fayemi a cikin kafafen yaɗa labarai.

Cewa aka riƙa yi wai Fayemi an ƙi amincewa da roƙon da ya yi na a datse kashi 10 cikin 100 na bashin.

Salsalar Wannan Hukuncin Biyan Bashi:

Batun wannan bashi da ake tankiya da tababar sa, ya samo asali ne daga wani hukuncin da kotu ta yanke cewa wasu ’yan kwangila da jami’an tuntuɓa na bin jihohi da ƙananan hukumomi 774 na ƙasar nan basussuka.

Wasu ’yan gidoga su ka yi iƙirarin cewa su jami’an tuntuɓa ne su ka ce sun taimaka wa ƙananan hukumoni da jihohi domin su karɓo kuɗaɗen su da aka cira fiye da kima tsakanin 1995 da 2002 domin biyan bashin Paris Club.

Wasu ‘yan kwangila kuma daga cikin su wai sun yi wa ƙananan hukumomi 774 ayyuka bashi, saboda zaman jiran tsammanin za a biya kuɗaɗen Paris Club a biya su daga ciki.

A baya PREMIUM TIMES ta buga labarin yadda Shugaban Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomin Najeriya, ALGON ya nuna goyon bayan a biya kuɗaɗen.

Buhari Ya Sani Ya Yi Shiru:

PREMMIUM TIMES ta buga labari a cikin Janairu, yadda Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya ta kai wa Shugaba Muhammadu Buhari ziyara tare da sanar da shi cewa cewa kada ya bari a biya kuɗaɗen, domin babu wata ƙwaƙƙwarar hujjar an yi ayyukan bashin.

Sai dai kuma duk da wannan gargaɗin Buhari bai taka wa su Malami burki ba

Sai ma da ta kai ga Malami ya samu saƙonnin gargaɗi daga wurare uku, ciki har da EFCC su na shaida masa cewa kada ya shiga gaba a biya bashin, domin akwai gidoga a cikin lamarin.

Cikin waɗanda su ka gargaɗi Minista Malami har da Shugaban ALGON na baya-baya, wanda shi ma ya nuna cewa kamfanonin tuntubar masu cewa su ne dillalan waɗanda ke bi bashi, ba su san da zaman su ba.

Yayin da su Malami su ka matsa lamba har Buhari ya sa hannu kan cakin kuɗin alƙawarin biya (promisory note), a ranar 4 Ga Disamba, 2020, su ma Gwamnomin daga baya cikin Janairu sun samo wani sabon umarni daga Buhari cewa kada a biya kuɗaɗen, har sai an yi ƙwaƙƙwaran bincike. Amma yanzu kuma Buhari ya amince a biya kuɗaɗen, ba tare da ya koma ta kan shawarar da Gwamnonin Najeriya su ka ba shi ba.

Ƙaryar Kwaram-kwaram Ta Ƙare:

Yanzu dai duk wani ƙoƙari da Gwamnonin Najeriya da Shugabannin ALGON 774 na Ƙananan Hukumomin Kasar nan kakaf su ka yi don kada a biya kuɗaɗen, ya tashi a iska, domin alƙalami ya bushe, tunda Shugaba Muhammadu Buhari ya sa hannun amincewa a biya kuɗaɗen.

Tags: AbujabashiBuhariGidigoGwamnoniHausaLabaraiNews
Previous Post

CIKAR JIGAWA SHEKARU 30: Badaru Ya Taka Rawar Gani, Daga Jaafaru M. Kaugama

Next Post

Hukumar tara Haraji ta Jihar Kaduna ta garkame wasu bankuna 4 saboda kin biyan tulin harajin naira miliyan N300.5

Next Post
Hukumar tara Haraji ta Jihar Kaduna ta garkame wasu bankuna 4 saboda kin biyan tulin harajin naira miliyan N300.5

Hukumar tara Haraji ta Jihar Kaduna ta garkame wasu bankuna 4 saboda kin biyan tulin harajin naira miliyan N300.5

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi
  • 2023: Ka zaɓi El-Rufai mataimaki, ‘ka yi nasara a zaɓe kamar yankan wuka’ – Kira ga Tinubu
  • RIKICIN PDP: Kwamitin Amintattun PDP ya tura wa Wike tawagar lallashi
  • KADUNA 2023: Uba Sani ya zaɓi Hadiza Balarabe mataimakiyar sa
  • ‘Yan bindiga sun kashe Sojoji 30, ‘yan sanda 10 da farin hula 12 a makon jiya

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.