Kwamitin Lura da Kuɗaɗen Gwamnantin Tarayya na Majalisar Tarayya ya nuna ɓacin rai ganin yadda Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari za ta ciwo bashin naira tiriliyan 5.62 domin narkawa a yi ayyukan raya ƙasa a kasafin 2021, amma kuma a gefe ɗaya hukumomin Gwamnantin Tarayya da yawa sun riƙe kuɗaɗen shiga sun ƙi zubawa a cikin Asusun Gwamnantin Tarayya domin a samu kuɗaɗen yin ayyuka.
Shugaban Kwamitin Kuɗaɗe na Majalisar Tarayya James Feleke ya ce, “a gaskiya ba mu jin daɗin yadda wasu hukumomin gwamnati ke riƙe kuɗaɗe ba su zubawa cikin asusun Gwamnanti, ita kuma gwamnati an bar ta fita gaganiyar ciwo basussukan da za ta yi ayyukan raya ƙasa.
“Don Allah ya zama wajibi mu tashi mu nuna kishin ƙasar mu don mu ci moriyar bunƙasar ta baki ɗayan mu.”
Feleke ya magana ne ganin yadda wasu hukumomin Gwamnantin Tarayya su ka kasa bada bayanai wasu kuma su ka ƙi zuba kuɗaɗen shigar su a Asusun Gwamnantin Tarayya tsawon lokaci.
Kwamitin dai na gayyatar Hukumomi ne ɗaya bayan ɗaya su na gabatar da bayanan kuɗaɗen shigar da su ke tarawa duk shekara, domin a ji yadda za a yi kirdadon kuɗaɗen shigar da za su tara daga shekarar 2022 zuwa 2024.
“Ɗaya daga cikin matsalar ƙasar nan ita ce rashin wadattattun kuɗaɗen shiga a aljihun gwamnatin tarayya. Dalili kenan Majalisar Tarayya ke son sanin adadin kuɗaɗen shigar da kowace hukuma ke tarawa a kowace shekara.” Inji Feleke
“Wasu ayyuka da dama da hukumomin gwamnati ke yi duk kashe maƙudan kuɗaɗe ne kawai ake yi a hanyar da ba ta cancanta ba. Kamata ya yi su daina bayar waɗannan manyan ayyuka na manyan kwangiloli, su maida hankali wajen tara wa Gwamnatin Tarayya kuɗaɗen shiga kawai.
Daga Feleke ya juya wajen Hukumar Sadarwa ta Ƙasa (NCC), inda ya umarce ta cewa ta gabatar da bayanan kuɗaɗen da ta tara tun daga shekarun 2018, 2019 da 2020.
Discussion about this post