Gwamna Aminu Masari na Jihar Katsina ya bayyana cewa a cikin Ƙananan Hukumomi 34 na jihar Katsina, jihohi 10 na fama da farmakin mahara masu garkuwa da mutane da satar dukiyoyi, a kowace rana.
Masari ya shaida wa Babban Kwamandan Askarawan Najeriya, Faruk Yahaya haka, a lokacin da ya kai masa jiyara a Katsina, ranar Alhamis.
Ya shaida masa cewa ‘yan bindiga su addabi ƙananan hukumomi 10 su na kisa, fyade, garkuwa da mutane, illatarwa, banka wa gidaje wuta da satar shanu.
Gwamna ya ce Gwamnatin Katsina ba ta gamsu da yanayin matsalar tsaron da ta dabaibaye jihar Katsina, tare da ya zama tilas a kawo ƙarshen lamarin.
“Mu na bukatar a samar da zaman lafiya cikin hanzari, domin sojoji su koma barikin su, su bar ‘yan, su kuma ‘yan sanda su karɓi aikin tsaron a hannun su.
Sannan kuma ya jaddada wa Shugaban Sojoji cewa Gwamnatin sa za ta ci gaba da bai wa sojojin Najeriya goyon baya, yadda za a kawar da matsalar tsaro.
A na sa jawabin, Janar Faruk ya shaida cewa ya kai ziyara Jihar Katsina domin ganawa da Sojojin Najeriya masu aikin tsaro a jihar domin ya gana dasu kuma ya ji daga bakin su halin da su ke ciki.
Daga cikin Ƙananan Hukumomi 10 da ‘yan bindiga su ke kai hare-hare, akwai Batsari, Jibiya, Sabuwa, Faskari, Safana da Ƙanƙara.
Discussion about this post