• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin APC na so jam’iyyar su ta gaggauta kiran taron gangami na ƙasa

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
August 11, 2021
in Manyan Labarai
0
‘Zan kawar da matsalar tsaro a Arewa’ –Sabon alwashin Buhari ga Gwamnonin Arewa

Gwamnonin jam’iyyar APC sun nemi a gudanar da taron gangami na ƙasa, domin a zaɓar wa jam’iyyar shugabanni, maimakon ci gaba da tafiya a hannun shugaban riƙo, Gwamna Mai-Mala Buni na Jihar Yobe.

Gwamnatin sun fitar da wanann matsaya ta su a cikin wata takardar bayan taron da su ka fitar a ranar Lahadi a Abuja.

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin APC, Abubakar Bagudu na Jihar Kebbi ne ya sa wa takardar hannu, kuma aka raba wa manema labarai a ranar Talata, a Abuja.

An dai naɗa kwamitin riƙon jam’iyya cikin 2020, a ƙarƙashin Gwamna Buni, bayan an tsige shugabancin Odams Oshiomhole.

Takardar sanarwar ta ce gwamnoni sun yi nazarin zaɓen shugabannin mazaɓu da APC ta yi a ranar 31 Ga Agusta. Don haka ta ce ci gaba da sauran zaɓukan a matakai, har a kai ga taron gangamin zaɓen shugabanni na ƙasa baki ɗaya.

Gwamnonin sun yaba tare da jinjina wa shugabancin su Buni musamman yadda aka samu nasarar gudanar zaɓen shugabannin mazaɓu na jam’iyyar lami lafiya, a cikin ruwan-sanyi.

Sun kuma nuna farin cikin yadda Kotun Ƙoli ta jaddada nasarar zaɓen Gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu.

Gwamnonin sun kuma ce sun yarda da shugabancin Mai-Mala Buni, ba kamar yadda wasu ke ta yaɗawa ba.

PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin yadda aka jibge jami’an tsaro a Hedikwatar APC a Abuja.

Sakataren Jam’iyyar APC na Ƙasa, John Akpanudoedehe ya bayyana cewa an jibge jami’an tsaro a Hedikwatar APC da ke Abuja ne domin ƙarfafa tsaro a ofishin na ƙasa.

Da ya ke ganawa da manema labarai a Abuja ranar Litinin, Akpanudoedehe ya ce babu wani abin nuna damuwa ko tayar da hankali.

Ya ce zaratan ‘yan sandan da aka jibge a hedikwatar da ke kan titin Balantire Street, kusa da Barcelona Hotel a Wuse 2 Abuja, an yi kawai domin ƙarfafa tsaro.

“An ƙaro ‘yan sanda ne domin su ƙara wa shugabancin Gwamna Mai-Mala Buni ƙarfin tsaro.

“A duk lokacin da ka tsinkayi alamomin wata matsala ko rahoton wata barazar tsaro, to abu na farko shi ne ɗaukar matakin gaggawa.

“Ba za mu taɓa bari wasu ‘yan tsiraru sun kunyata mu ba, saboda mu ne ke riƙe da gwamnati a ƙasar nan. dalili kenan mu ka ɗauki matakan kariyar duk wata shegantakar da ka iya bijirowa.

“Mun samu rahoton sirri na jami’an tsaro. Don haka ba zai yiwu mu ɗauko ‘yan iska da ‘yan jagaliya su zo su kare Sakateriyar APC ta Ƙasa a Abuja ba. Abin da ya dace shi ne mu sanar wa ‘yan sanda da SSS. Kuma hakan mu ka yi.” Inji Akpanudoedehe.

Idan ba a manta ba ita ma APC ta shiga ruɗani, yayin da wasu jiga-jigan ta su ka nemi Shugaban Riƙo Gwamna Buni ya sauka, domin dokar ƙasa ba ta yarda Gwamna ya riƙe wani muƙami ba.

PREMIUM TIMES Hausa ta buga rahoton da Karamin Ministan Ƙwadago, Festus Keyamo ya yi gargaɗin cewa mulki zai suɓuce daga hannun APC idan Gwamna Buni ya ci gaba da shugabancin jam’iyyar ko na tsawon sati ɗaya ne.

Ƙaramin Ministan Ƙwadago, Festus Keyamo, ya gargaɗi jam’iyyar APC cewa akwai gagarimar matsalar da ta tunkari jam’iyyar, matsawar Gwamna Mai Mala-Buni na Jihar Yobe ya ci gaba da kasancewa Shugaban Jam’iyya na Riƙo har zuwa jibi Asabar, ranar zaɓe shugabannin APC a matakan Kananan Hukumomi da Jihohi da za’a yi ranar 31 Ga Yuli.

Yayin da ya aika da wata wasiƙar gaggawa ga jam’iyya s asirce, wadda ta faɗo hannun PREMIUM TIMES, Keyamo wanda shi ma gogaggen lauya ne, ya bayyana haramcin riƙe APC da Gwamna Buni ke yi, domin Dokar Ƙasa da Dokar APC sun haramta Gwamna ya riƙe wani muƙami ko shugabanci banda na gwamna da aka rantsar da shi don ya riƙe.

Wannan mahaukaciyar guguwa ta taso ne sanadiyyar hukuncin da Kotun Ƙoli ta Yanke, inda ta jaddada nasarar Gwamna Rotimi Akeredolu na Ondo, na APC, kan Eyitayo Jegede na PDP.

Yadda Sakacin Lauyoyin Jegede Ya Bai Wa Akeredolu Nasara A Ɓagas:

Keyamo ya ce Jegede ɗan takarar PDP ya shigar da Gwamna Akeredolu ƙara, bisa zargin zaɓen da bai cancanta ba, domin a lokacin da aka yi zaɓen cikin Oktoba 2020, Gwamna Mala Buni ne Shugaban Riƙon APC, wanda haramun ne a Dokar Ƙasa Sashe na 183 na 1999 Gwamna ya riƙe wani muƙami daban da na Gwamna.

Haka ma Dokar APC Sashe na 17 ya haramta wa Gwamna riƙe wani muƙami lokacin da ya ke kan mulki.

“Inda Jegede da lauyoyin sa su ka kwafsa shi ne da ba su haɗa da sunan Gwamna Mala Buni Shugaban Riƙon APC tare da na Gwamna Rotimi sun maka su kotu tare ba.

“Da an haɗa da sunan Shugaban Riƙon APC, to da a ranar Litinin Kotun Koli ta soke zaɓen ta bai wa Jegede na PDP nasara.” Inji Keyamo.

A kan haka ne Keyamo ya bada shawarar cewa lallai kamata ya yi a ɗage zaɓen shugabannin APC na Ƙananan Hukumomi da na Jihohi da aka shirya gudanarwa a ranar Asabar mai zuwa.

“Domin banda Mai Mala-Buni, akwai Gwamnonin Osun da na Neja a cikin Kwamitin Amintattun APC, waɗanda su ma bai kama ta a saka su a ciki ba.

Ya ce idan aka yi zaɓen shugabannin jam’iyya a ƙarƙashin Buni, to duk wanda ya ci zaɓe a ƙarƙashin APC, tun daga kan kansila har shugaban ƙasa sai kotu ta ƙwace kujerar sa.

A kan haka ne ya bada shawara a ɗage zaɓe na shugabannin ƙananan hukumomi da na Jihohi. Sannan a gaggauta cire Mala Buni, ta hanyar taron Majalisar Zartaswar APC na gaggawa, wanda zai cire waɗannan shugabannin riƙo, ya naɗa wasu.

Gwamna Rotimi ya tsallake rijiya ne saboda Alƙalai huɗu daga cikin bakwai ne su ka yarda da zaɓen sa bisa dalilin cewa sun yarda Gwamna Buni bai cancanci riƙe jam’iyya ba, amma mai ƙara fa bai shigar da Buni a cikin ƙarar da ya shigar ba.

Sauran lauyoyi uku kuwa su ka ce ba sai an sha wahalar shigar da sunan Buni ba, tunda dai bai cancanci shugabancin APC ba, to Gwamna Rotimi bai ci zaɓe ba ƙarƙashin APC kenan.

A kan haka ne Keyamo ya ce wannan shari’a ta nuna kenan duk wanda zai kai ƙarar APC nan gaba, to matsawar ya haɗa da sunan Buni, ko tantama babu nasara zai yi a kotu.

Tags: AbujaAPCEl-RufaiGwamnoniHausaKadunaLabaraiNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

DAMBARWAR SHUGABACIN PDP: Za a yi taron gangami cikin Oktoba, yayin da Secondus ya tsallake ramin tsigewa

Next Post

Ƙasashen Turai fatali su ke yi da fiye da kashi 76% na amfanin gonar da ake nomawa a Najeriya -FOA

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Muna rokon gwamnati da ta gaggauta samar wa ‘yan Najeriya sauki akan matsanancin tsadar abinci da ake fama dashi a kasa

Ƙasashen Turai fatali su ke yi da fiye da kashi 76% na amfanin gonar da ake nomawa a Najeriya -FOA

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Dalilin da ya sa INEC ta yi wa kotu jayayyar kwafe-kwafen bayanan da Atiku da Obi su ka gabatar – Lauyan INEC
  • HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru
  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Kotu ta zare wa lauyoyin Peter Obi idanu, saboda ɓata lokaci wurin sauraren ƙararraki
  • RAƊAƊIN CIRE TALLAFIN FETUR: ‘Dama can babu ba a ware kuɗin tallafin fetur a Kasafin Kuɗin 2023 ba’ – Kyari, Shugaban NNPCL
  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Tinubu da INEC sun ƙi amincewa da tulin kwafe takardun da Atiku ya kwafo daga iReV

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.