Hukumar Hana Bazuwar Cututtuka ta Ƙasa (NCDC) ta bayyana cewa zuwa ranar 1 Ga Agusta, 2021, mutum 31,425 su ka kamu da cutar amai da gudawa, ko kuma kwalara, yayin da cutar ta kashe mutum 1000 a cikin wannan shekara.
Sai dai kuma binciken da PREMIUM TIMES ta gudanar a wasu garuruwa da ƙauyuka da lungunan cikin jihohi 22, ya nuna lamarin ya yi munin da ya wuce hasashen da Gwamnatin Tarayya ta bayyana, nesa ba kusa ba.
PREMIUM TIMES Hausa ta bi diddigin rahotannin, ta tsakuro wasu dalilan da ke haddasa ɓarkewar amai da gudawa a cikin al’umma, musamman inda babu ingantattun ababen rayuwa.
Cikin jihohin da PREMIUM TIMES ta bi diddigi sun haɗa da Kano, Jigawa, Katsina, Zamfara, Sokoto, Kebbi, Benuwai, Filato, Ebonyi da Enugu.
1. Rashin tsafta da barin ƙazanta a gida, musamman abinci da kayan abinci ko kwanukan cin abinci.
2. Zubar da tulin shara da bola aikin unguwanni, wadda ruwan sama ke maida ƙazantar ta s cikin jama’a.
3. Zubar da shara ko bola ko bayan gida a cikin ƙaramu da magudanan ruwa.
4. Yin bayan gida a fili ko a kan bola.
5. Rashin ruwa mai tsafta a cikin al’umma.
6. Ƙarancin asibitocin kula da marasa lafiya a cikin jama’a marasa galihu.
7. Ƙaranci ko rashin magungunan da za a bai wa mai cutar kwalara cikin gaggawa.
8. Matsalar ƙarancin jami’an kiwon lafiya a cikin jama’a.
9. Rashin hanyoyi masu kyau da za a garzaya asibiti da mai cutar amai da gudawa cikin gaggawa.
10. Shan ruwan ƙarama ko kogi, wanda ake zubar da shara, kashin dabbobi da kuma bayan gida.
Discussion about this post