• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari Travelling

    Duk da tsananin hare-haren da ya darkaki Najeriya a kwanakin nan Buhari zai waske taro Dakar

    An cika sansani uku fal da tubabbun ‘yan Boko Haram -Gwamna Zulum

    An cika sansani uku fal da tubabbun ‘yan Boko Haram -Gwamna Zulum

    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari Travelling

    Duk da tsananin hare-haren da ya darkaki Najeriya a kwanakin nan Buhari zai waske taro Dakar

    An cika sansani uku fal da tubabbun ‘yan Boko Haram -Gwamna Zulum

    An cika sansani uku fal da tubabbun ‘yan Boko Haram -Gwamna Zulum

    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

ƊAN BINDIGA KAMAR WANI SARKI: Gogarman daji ya gindaya wa Gwamnatin Katsina sharuɗɗan daina kai hare-hare

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
August 28, 2021
in Babban Labari, Rahotanni
0
Ƴan bindiga sun sace mutum 60 a Rini jihar Zamfara

A daidai lokacin da Arewa ke ƙara dulmiya a hannun ‘yan bindiga, a Jihar Katsina wani gogarman masu garkuwa da mutane mai suna Usman Idris da aka fi sani da Ruga Kachallah, ya nemi a biya shi diyyar dukkan buhunan hatsin sa da jami’an ‘yan sanda su ka banka wa wuta, kafin a yi sulhu da shi.

Sai dai kuma Rundunar ‘Yan Sandan Katsina ta yi watsi da kalaman na sa, inda ta bayyana cewa sau huɗu ana sulhu da Ruga Kachallah, amma sai ya tayar da tubar sa.

Kachallah shi ne babban gogarman ‘yan bindigar da ka hana Ƙaramar Hukumar Safana zaman lafiya da kewayen ta a Jihar Katsina, kamar yadda PREMIUM TIMES ta tabbatar.

Mazauna yankunan sun shaida wa wannan jarida cewa akwai dandazon ‘yan bindigar da ke ƙarƙashin Ruga Kachallah, waɗanda sun fitini garuruwa da ƙauyukan yankin da garkuwa da satar shanu da dukiyoyi masu tarin yawa, gaba-gaɗi.

Sai dai kuma wannan jarida ta ji cewa Kachallah ya na sana’ar da ta sa ya ke da farin jini sosai a garuruwan da ke kewayen Safana.

Ya mallaki motocin haya sosai waɗanda ake yi masa jigila garuruwan yankin ana tara masa kuɗaɗe.

Wannan sana’a da Kachalla ke yi ta samar wa matasa da dama aikin yi a kewayen. Kuma su na hamdala sosai ga Kachallah.

Kachallah: Ɗan Bindiga Kamar Ɗan Sarki:

Mutanen karkarar Rulumbusawa, Yartsaku, Maƙera, Gimi da Chirena da ke cikin Ƙaramar Hukumar Safana a Jihar Katsina, sai sun nemi iznin Kachallah kafin su fita zuwa gonakin su.

A Arewacin Runka, gari na biyu wajen girma a Ƙaramar Hukumar Safana, can ma manoma sun miƙa wuya ga ‘Daular Kachallah’, gogarman ‘yan bindiga.

Kachallah Da Gwamnatin Katsina: Kar-Ta-San-Kar:

Ba kamar sauran ‘yan bindigar da ke ɓoye a cikin daji ba, shi Ruga Kachallah a cikin garin Gimi ya ke zaune da iyalin sa. Ya san kowa, kowa ya san shi.

Kwanan nan mazauna garin sun hana jami’an ‘yan sanda kama wani yaron sa, wani ɗan ta-kife, mai suna Gulbi.

An ce Kachallah na bai wa Gulbi shanun da ya sato, shi kuma ya na sayar masa.

Lokacin da mazauna garin su ka hana ‘yan sanda kama Gulbi, sun shaida wa Kwamandan Eriyar Safana, Dutsin-Ma, Ɗanmusa, Kurfi da Batsari, Aminu Umar-Daye cewa, ba za su bari a kama Gulbi ba, saboda idan aka kama shi, Kachalla cewa zai yi da haɗin bakin jama’a aka kama Gulbi, kuma a kan su zai huce haushin sa.

Haka dai Umar Daye ya haƙura ya janye ‘yan sandan.

Sai dai kuma a ranar 25 Ga Mayu, jami’an tsaro sun koma har gidan Kachalla, ba su same shi ba, amma sun banka wa gidan wuta, su ka ƙone masa buhunan kayan abinci. Sannan kuma su tafi da matan sa biyu.

Sai dai kuma ‘yan garin sun yi taron-dangi sun kashe wutar.

Daga nan fa Kachalla ya fusata, ya riƙa kama mutane, har sai da aka sakar masa mata biyu sannan ya saki wani malamin firamare da ya damƙe. Kuma ya ƙara ƙaimi sosai wajen kama mutane ya na yin garkuwa da su, ana biyan sa diyya.

Sulhun Da Bai Tsinana Komai Ba:

Cikin 2016 ne Riga Kachalla ya haɗa kai da wasu fitinannun ‘yan bindiga da su ka haɗa har da Abdullahi Karki, wani tubabben ɗan bindiga a yanzu, su ka yi alƙawarin ajiye makamai a wani ƙwarya-ƙwaryan bikin karɓar tubar su a ƙarƙashin Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Mustapha Inuwa. An yi bikin a ƙauyen Illela, cikin Ƙaramar Hukumar Safana.

Sai dai kuma ba a daɗe da yin sulhun ba, sai dakarun Kachalla su ka koma bakin aikin kama mutane, su na yin garkuwa da su, ana biyan Kachalla kuɗaɗen fansa.

Bayan jami’an tsaro sun matsa lamba, wani dakaren Kachalla mai suna Jummah Tambai, ya kwashe iyalin sa ya koma Jihar Nassarawa, daga can kuma aka ce ya koma wani wurin da ake haƙar ma’adinai a cikin dajin Jihar Osun.

Haka shi ma mahaifin Kachalla da ke zaune a ƙauyen Sulluɓawa cikin Ƙaramar Hukumar Safana, ya yi hijira ya koma garin Banki cikin Ƙaramar Hukumar Anchau, saboda ya kasa hana ɗan sa Kachalla ci gaba da fashi, hare-hare da garkuwa da mutane.

Wanda Ya Saba Da Lale Miliyoyin Kuɗin Fansa, Ba Ya Son Bari Saboda Gudun Talauci – Na-Ammee, Tubabben Ɗan Bindiga:

A tattaunawar PREMIUM TIMES Hausa da wani tubabben ɗan bindiga mai suna Na-Ammee, wanda abokin Kachalla ne, ya ce ya yi ƙoƙarin shawartar Kachalla ya daina kai hare-hare, domin hana manoma zuwa gona zai haifar da tsadar abinci, kuma ya na ƙuntata wa mutanen yankin mahaifar sa.

“Da wahala mutanen da su ka saba da lale miliyoyin kuɗaɗen fansa su na ƙirgawa, su dawo irin rayuwar su ta fama da rashi.

“Yanzu ni ɗin nan da na tuba na daina, yanzu haka ina tunanin na sayar da tsohon babur ɗi na domin na samu kuɗin noma gonaki na.” Inji Na-Ammee.

Abin Da Ya Sa Na Ke Garkuwa Da Mutane -Kachalla:

PREMIUM TIMES ta samu tattaunawa da Gogarman Daji Kachalla ta wayar tarho, inda ya amsa laifin hare-haren da ake cewa ya na kaiwa.

“Ni da duk abin da aka gaya maka ina yi, ko ka ji ana cewa na yi, to duk ma aikata. Amma ina yi ne saboda dalili.

“Jami’an tsaro sun kama yara na huɗu da mata na biyu, kuma su ka ƙona min hatsi har buhu 100.”

Kachalla ya ce idan ana so ya daina, tunda an saki matan sa, to a saki sauran yaran sa huɗu, kuma a biya shi diyyar buhunan hatsin sa 100 da ‘yan sanda su ka banka wa wuta. Ya ce kowane buhu ɗaya ya tashi a kan naira 30,000.

“Saboda buhuna 160 na noma. Bayan na fidda zakka lokacin Ramadan, na yi saura buhu 100, wanda Area Kwamanda na ‘Yan Sandan Dutsin-Ma ya zo su ka banka wa wuta, kuma ya kama mata na biyu.

“A lokacin na kira lambar wayar Area Kwamanda ɗin, amma bai ɗaga ba, saboda ya san abin da ya yi min. Kuma na kira Hakimin Safana da Shugaban Ƙaramar Hukumar Safana duk na sanar da su, amma ba su yi komai ba.”

“Da na ga sun ƙi sakin matan, ni kuma sai na kama wani malamin makaranta, na ƙi sakin sa, har sai da aka saki matan nawa su biyu tukunna.

“Amma dai har yanzu ina neman a biya ni diyyar hatsi na buhu 100 da aka ƙone ƙurmus.” Inji Kachalla.

“Raina Min Wayau Aka Yi A Wurin Sulhu, Shi Ya Sa Na Tayar Da Tuba” -Kachalla:

“Ina cikin waɗanda aka yi zaman sulhu da su a Katsina. Amma sai ba a kula da ni yadda ya kamata ba. Aka damƙa min wani akwalar babur, su kuma wasu da su ka tuba din aka yi masu hidimar da ta fi wadda aka yi min yawa. To ka dai ji dalilin tada tubar da na yi” Inji Kachalla.

Kakakin ‘Yan Sandan Katsina, Gambo Isa ya ce ba za su amince da sharuɗɗan da Kachalla ya gindaya ba.

“Saboda sau huɗu ana yin sulhu da shi, amma ya na tada tuba.

Tags: AbujaHausaLabaraiNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

GARDAMAR KWALLON KAFA: Ɗan giya ya kashe ɗan Arsenal

Next Post

Korona bata ɗaga wa ƴan Najeriya ƙafa ba ranar Juma’a mutum 10 ta yi ajalin rayukansu cikin har da tsohon sanata

Next Post
KORONA MAI SAURIN KISA: Ta kashe mutum 7, ta kama mutum 1,149 a ranar Laraba

Korona bata ɗaga wa ƴan Najeriya ƙafa ba ranar Juma'a mutum 10 ta yi ajalin rayukansu cikin har da tsohon sanata

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • KOWA TA SA TA FISSHE SHI: Ƙoƙarin haɗewar LP da NNPP ya kakare, Peter Obi zai bayyana mataimakin takarar sa ranar Juma’a
  • ‘Da gangar aka bari ƴan bindiga suka kai harin gidan yarin Kuje, saboda na yi ta faɗin hakan zai auku – Mamu
  • Ƴan bindiga sun babbake cibiyoyin kiwon lafiya sun yi dalilin dole aka rufe wasu 69 a Katsina
  • Dala ta ƙara kekketa wa naira rigar mutunci daidai lokacin tsadar kayan abinci
  • Duk da tsananin hare-haren da ya darkaki Najeriya a kwanakin nan Buhari zai waske taro Dakar

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.