• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe – Nazarin DUBAWA

    INEC ba za ta rufe rajistar zaɓen 2023 a ƙarshen Yuni ba – Farfesa Yakubu

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Teacher

    Gwamnati ta umarci makarantu su fara amfani da Tsarin Ƙara wa Malamai Shekarun Ritaya

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun damke dan shekara 30 din da ya nemi yi wa dattijiya mai shekaru 75 fyade

    Petrol Tankers

    ƊAN KUKA MAI JA WA UWAR SA JIFA: Ƙungiyar IPMAN ta ce ba za ta iya ci gaba da sayar da fetur a garuruwan yankin Igbo ba

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe – Nazarin DUBAWA

    INEC ba za ta rufe rajistar zaɓen 2023 a ƙarshen Yuni ba – Farfesa Yakubu

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Teacher

    Gwamnati ta umarci makarantu su fara amfani da Tsarin Ƙara wa Malamai Shekarun Ritaya

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun damke dan shekara 30 din da ya nemi yi wa dattijiya mai shekaru 75 fyade

    Petrol Tankers

    ƊAN KUKA MAI JA WA UWAR SA JIFA: Ƙungiyar IPMAN ta ce ba za ta iya ci gaba da sayar da fetur a garuruwan yankin Igbo ba

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Yadda yunwa ke ƙara ruruta wutar matsalar tsaro a yankin Barno, Yobe da Adamawa

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
July 31, 2021
in Harkokin Kudade/Noma
0
IDP in Borno State

IDP in Borno State

Hujjoji da dalilai masu tabbatar da barazanar yunwa na ƙara darkakar mutum miliyan 4.4 a yankin, waɗanda a cikin su yanzu haka mutum sama da 775,000 ba su da abincin yau ballantana na gobe, kuma babu siɗi balle saɗaɗa.

Amina Adamu mai shekaru 25 ta saba da yunwa, ta zame mata jiki, domin tare su ke kwana su na tashi babu ranar raba wannan ƙawancen tilas da su ka ƙulla.

Ta kan shafe kwanaki babu abinci. Wasu lokuta kuma ta kan shafe wata ɗaya ta na ɗan cin lomar tuwon nan da ake kira ci-kar-ka-mutu.

A cikin ‘yar bukkar da ta ke kwana a Sansanin Masu Gudun Hijira na Elmiskin da ke Jere kusa da Maiduguri, a Jihar Barno, Amina na ɗaya daga cikin ɗimbin waɗanda ke kwana su na tashi da yunwa sanadiyyar ƙarancin abinci.

Na Shafe Shekaru 5 Ina Dogaro Da Abincin Agaji, Shi Ɗin Ma Yanzu Na Kai Wata Uku Ban Samu Ba -Amina

Amina ta shaida cewa ta shafe shekaru biyar ta na dogaro da abincin agaji. To ƙarin abin da ya firgita mata rayuwa shi ne yanzu haka an kai watanni uku kenan, abincin agajin ma ya faskara.

A yanzu a sansanin, mata masu juna biyu da masu shayar da jira-jirai ne kaɗai ake bai wa abincin agaji da jinƙai.

Mazauna Sansanonin Masu Gudun Hijira irin su Amina da dama sun dogara ne kan ɗan abincin agaji da tallafin da ake bayarwa.

Shi ɗin ma ya na samun cikas saboda yawan kai wa ‘yan ƙungiyoyin agaji hare-hare an kashe wasu, sannan kuma an yi garkuwa da wasun su. Wannan ya na haifar da cikas da tsaiko wajen raba wa mabuƙata abincin tallafi a sansanonin masu gudun hijira.

Yadda Ƙaddarar Zaman Sansanin ‘Yan Gudun Hijira Ta Ritsa Da Ni -Amina:

“Shekaru biyar da su ka gabata Ni da miji na sun tsere daga Bama, garin da ke da babban sansanin sojoji kusa da kan iyakar Najeriya da Kamaru. Mun gudu ne yayin da Boko Haram su ka kai mana wani mummunan hari.”

Irin wannan mummunan hari na kisan-wulaƙanci da ‘yan ta’adda ke yi, ya haddasa sama da mutum miliyan 8.7 sun arce sun bar gidajen su, babu shiri, kuma babu ranar komawa, a jihohin Barno, Yobe da Adamawa.

“Mu na kwance da dare mu na cikin barci, kawai sai mu ka fara jin ƙara da rugugin harbin bindigogi. Daga nan fa duk mu ka tsere mu ka yi tafiyar sa’o’i shida a ƙasa. Daga nan mu ka samu motar da ta kai mu Bama, ta sauke mu a tasha.

“Washegari da safe mu ka fara bara domin su samu kuɗin da za mu biya direban da ya ɗauko mu ɗin.” Inji Amina.

Iyalai da yawa sun dogara da noma domin ciyar da kan su da ‘ya’yan su, kamar yadda su ma su Amina da noman su ka dogara.

Amma hare-haren ta’addancin dhcake yi wa manoma ya haifar da tsoro har manoma sun daina zuwa gona. Zaɓi ya rage wa manomi. Ko dai ya tafi gona a sace ko a tsinto gawar sa, ko kuma ya zauna ya rungumi yunwa, ya tsira da ran sa.

Irin wannan mawuyacin hali da manoma su ka shiga a yankunan da tashe-tashen hankula ya yi ƙamari ne ya haddasa bala’in ƙarancin abinci.

“A yanzu mu na ɗinka huluna ne domin samun ɗan taro da sulai. Abin da mu ke yi kenan domin samun ɗan kuɗin kashewa akwai-ya-babu.” Inji Amina.

Yadda Boko Haram Su Ka Yanke Min Rayuwar Jin Daɗi, Na Dawwama Cikin Ƙuncin Rayuwa -Aisha Idris:

Aisha Idris ita ma kamar Amina, matar aure ce mai ‘ya’ya uku wadda ke zaune tare da mijin ta a garin Baga, gari mai albarkar hada-hadar kasuwancin kifi a kusa da Tafkin Chadi. Sai dai kuma rayuwar jin daɗin da su ke ciki ta yanke, a ranar da Boko Haram su ka kai wa garin hari, cikin 2015.

Tun daga waccan rana har zuwa yau tsawon shekaru shida, A’isha na fama da rayuwar ƙuncin da babu ranar fita a cikin ta.

A ranar da aka kai masu farmakin ta rasa yara huɗu, an kashe su. A haka su ka tsallake su ka gudu, su ka bar ‘yan dabbobin su da harkokin kasuwancin kifin da su ke yi duk su ka tsallake su gudu.

A yanzu A’isha na zaune a ɗaya daga cikin Sansanin Masu Gudun Hijira mafi girma a jihar Barno, inda ta ke rayuwa bisa dogara da abincin tallafin da Ƙungiyar Tallafin Abinci ta Duniya (WFP) ke rabawa. WFP bangare ne na Majalisar Ɗinkin Duniya.

“Ina godiya da irin tallafin da WFP ke ba ni na abinci tun daga lokacin da na samu ciki.

“Domin mu samu abincin da ake ba mu ya riƙa isar mu, idan an ba mu na safe, mu kan ajiye mu haɗa da na rana mu ci. Ko kuma mu ajiye na rana, mu haɗa shi da na dare mu ci, don ya ishe mu.” Inji A’isha.

A’isha wadda a Baga su ke da yalwa da wadatar da har maƙwauta su ke cuyarwa, sai aka wayi gari sun shafe shekaru shida kenan a sansanin da su ma abincin sai an tallafa masu.

Rayuwar Tsaka-mai-wuya: Ka Zauna Cikin Yunwa Ko Ka Saida Rai Ka Tafi Gona Ka Rasa Rai:

Ba ma harsashen bindiga ne kaɗai ke kashe mutane ba ko jefa su cikin ƙunci da muwuyacin hali. Bala’in yunwa kaɗai ya isa kashe mutum a yankin, ko ya nukurkusar da shi, ta yadda ba zai iya amfana wa kan sa komai ba, saboda rashin ƙarfi, sai dai ya dogara da tallafin abinci kaɗai a rayuwar sa.

Babu wanda zai iya faɗa da mai ɗauke da bindiga alhalin ya na fama da yunwar shekaranjiya da ta jiya, har ma da ta yau a cikin sa.

Ta kai ga hatta mutanen da ke zaune a sansanonin amai gudun hijira ana kai masu hari. Idan su ka koma gaeuruwa ko ƙauyukan da su ma abincin ba isar su ya yi ba, duk sai yunwa ta rafke su, babu mai iya tayar da wani. To irin wannan rayuwa ce miliyoyin mutane ke yi a wannan yanki.

Annobar korona ta ƙara ruruta matsalar sosai, musamman wajen tsaikon kasa kai kayan abincin tallafi a yankuna ko kuma matsalar sayen kayan abincin da ya kamata a raba masu.

Sai dai yanzu sosai Majalisar Ɗinkin Duniya da sauran ƙungiyoyin bayar da tallafi da agaji su na ci gaba da haɗa ƙarfi dare da rana domin tabbatar da cewa al’umma waɗanda ke cikin wannan halin ƙunci su na samun wadataccen abincin da za su ci su rayu.

Tags: AbujaHausaNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Saraki ya shiga hannu, EFCC na tuhumar sa a Abuja

Next Post

Ƴan Najeriya sun yi tir da yadda ɗan majalisan da ya maida mutanen sa kamar kaji, yana watsa musu kudi suna warwaso

Next Post
Ƴan Najeriya sun yi tir da yadda ɗan majalisan da ya maida mutanen sa kamar kaji, yana watsa musu kudi suna warwaso

Ƴan Najeriya sun yi tir da yadda ɗan majalisan da ya maida mutanen sa kamar kaji, yana watsa musu kudi suna warwaso

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ‘Ga mu nan tafe, duk inda kuke za mu kutsa mu yi ragaraga da ku” – Sakon Buhari ga ‘yan bindigan da suka kai harin Shiroro
  • Wike ya nuna Ko-In-Kula ga tawagar sulhu da Atiku ya aika masa can kasar Turkiya in da yake hutu
  • RIKICIN PDP: Yadda ƙwararrun masu tsaron gida ke neman hana Atiku cin bugun ‘fanaritin sa’ na ƙarshe
  • TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki
  • ƘORAFE-ƘORAFEN MANYAN PDP KAN ATIKU: ‘Zan bi su gida-gida ina sasantawa da su’ – Inji Atiku

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.