• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Crisis in Jos

    BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

    GUDUN YIN BIYU-BABU: Gwamnan Bauchi ya sayi fam ɗin sake yin takarar gwamna, daidai lokacin da ya fito takarar shugaban ƙasa a PDP

    Farin jinin Buhari da mara min baya da yayi ya sa na samu daukaka a siyasa – Bala Mohammed

    Kano State Assembly

    Dan majalisar dokoki na jihar Kano ya doka ‘Ribas’ bayan ya tsunduma lambun jam’iyyar NNPP, ya ya rungumi tsintsiyar sa ya dawo APC

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Crisis in Jos

    BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

    GUDUN YIN BIYU-BABU: Gwamnan Bauchi ya sayi fam ɗin sake yin takarar gwamna, daidai lokacin da ya fito takarar shugaban ƙasa a PDP

    Farin jinin Buhari da mara min baya da yayi ya sa na samu daukaka a siyasa – Bala Mohammed

    Kano State Assembly

    Dan majalisar dokoki na jihar Kano ya doka ‘Ribas’ bayan ya tsunduma lambun jam’iyyar NNPP, ya ya rungumi tsintsiyar sa ya dawo APC

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

RAJISTAR ZAƁE A YANAR GIZO: Yadda matasa da ɗalibai su ka fara rige-rigen rajista a matakin farko – Shugaban INEC

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
July 16, 2021
in Babban Labari, Rahotanni
0
INEC: Mutum 542,576 sun yi rajistan zabe ta hanyar CVR a yanar gizo

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa jimillar ‘yan Najeriya 542, 576 ne su ka kammala matakin farko na yin rajistar katin zaɓe (CVR) a yanar gizo da ake gudanarwa yanzu ya zuwa ƙarfe 7 na safiyar ranar Litinin, 12 ga Yuli, wato mako biyu cif daga lokacin da aka fara aikin.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmud Yakubu, shi ne ya bayyana haka a ranar Talata lokacin da ya yi taro a Abuja da Zaunannun Kwamishinonin Zaɓe (RECs).

Yakubu ya ce hukumar ta na farin ciki da nasarar da ake samu a matakin farko na yin rajista a yanar gizo a dukkan faɗin ƙasar nan, wanda aka fara a ranar Litinin, 28 ga Yuni.

Ya ce, “Da farko, mun riƙa ba ‘yan Nijeriya bayani kan yadda aikin ke wakana a kowace rana. Kuma mun yi alƙawarin bada cikakkun bayanai na mako-mako, wanda mu ka fara a ranar Litinin ta makon jiya.

“Ya zuwa ƙarfe 7 na safiyar jiya Litinin, wato mako biyu cif tun da aka fara aikin, an samu jimillar ‘yan Nijeriya 542,576 da su ka kammala matakin farko na yin rajista a yanar gizo.

“Daga cikin waɗannan ɗin, mutum 456,909 sababbin masu rajista ne yayin da mutum 85,667 sun nemi a yi masu sauyin wurin yin zaɓe ne ko sauya katin zaɓe ko ɗora ƙarin bayani kan katin su.

“Haka kuma hukumar ta yi ƙoƙarin sama wa ‘yan Nijeriya bayanai kan yadda ake karkasa masu zaɓe a duk jihohin ƙasar nan ta fuskar shekarar haihuwa, sana’a, jinsi da kuma naƙasa.

“Daga cikin mutum 542,576 waɗanda su ka yi rajista a yanar gizo zuwa yanzu, mutum 356,777 (wato kashi 66 cikin ɗari) matasa ne ‘yan tsakanin shekaru 18 zuwa 34. Masu bi masu su ne mutum 134,719 ‘yan tsaka-tsakin shekaru waɗanda su ka kasance ‘yan shekaru daga 35 zuwa 49.

“Kashi na uku su ne masu nisan shekaru, wato ‘yan 50 zuwa 69 waɗanda a cikin su mutum 44,896 ne su ka yi rajista. Abin sha’awa, an samu dattawa 6,184 ‘yan shekaru 70 zuwa sama da su ka yi amfani da damar rajista a yanar gizo su ka yi rajistar su ma.

“A dangane da karkasa masu zaɓe bisa sana’a, mutum 156,446 ɗalibai ne; 38,217 masu sana’ar hannu; 24,421 manoma da masunta; 150,145 ‘yan kasuwa da masu tireda; 35,831 ma’aikatan gwamnati, sai kuma matan aure 8,334. Sauran 129,182 da su ka yi rajista kuma ba su faɗi sana’o’in su ba.

“Dangane da jinsi, mutum 321,781 maza ne, yayin da 220,795 mata ne.

“A ƙoƙarin mu na yi wa dukkan ‘yan Nijeriya aiki yadda ya kamata, hukumar ta buƙaci masu son yin rajista da su riƙa nuna irin naƙasar da su ke da ita (idan akwai). Hakan zai taimaka mana wajen kawo kayan aikin da su ka dace da su irin su na’urar Braille da za ta jagorance su wajen zaɓe da kuma madubin ƙara girman rubutu saboda masu buƙatar musamman a ranar zaɓe.

“Ya zuwa yanzu, mun samu bayanan masu rajista mutum 6,558 waɗanda su ka bayyana irin naƙasar da su ke da ita.”

Yakubu ya ce bayanan da ake da su na jihohi da karkasuwar sana’o’i an zuba su a gidan yanar hukumar da filayen ta na soshiyal midiya.

Haka kuma ya bayyana cewa hukumar ta amince da cibiyoyin yin rajistar ganin ido da ido guda 811, daga ranar 19 ga Yuli, domin hukumar na sane da cewa ba ko wane ɗan Nijeriya ba ne ya ke da komfuta ko babbar waya ko kuma damar shiga intanet da har zai yi rajista ta hanyar yanar gizo.

“Burin mu shi ne mu farfaɗo da cibiyoyi 2,673 inda za mu tura ma’aikata 5,346 domin yi wa mutane rajista ido da ido.

“To amma kuma bayan mun tattauna da masu ruwa da tsaki, hukumar ta yanke shawarar za ta ci gaba da aiki daki-daki ne yayin da mu ke nazarin yanayin tsaro a faɗin ƙasar nan.

“Mu da masu ruwa da tsaki, ciki har da hukumomin tsaro, mun amince cewa mu fara daga ofisoshin mu na jihohi da na ƙananan hukumomi.

“Wannan na nufin za a fara da wurare 811 a faɗin ƙasar nan, wanda ya ƙunshi ofisoshin da ke jihohi 37 da yankin Abuja da kuma yankunan ƙananan hukumomi guda 774.

“Mun tanadar da na’urori tare da tura su faɗin ƙasar nan don ci gaba da koyar da jami’ai don shirin fara yin rajistar ido da ido.”

Ya ƙara da cewa jerin sunayen cibiyoyin guda 811, haɗi da inda su ke da kuma layukan tarho da aka tanadar wa kowane ofishin jiha ko ƙaramar hukuma a faɗin ƙasar nan, duk an wallafa su a gidan yanar INEC da shafukan ta na soshiyal midiya saboda ko wani zai yi tambaya.

“Hukumar ta na sane da cewa mun shirya fara aikin rajistar ido da ido a ranar Litinin, 19 ga Yuli. Sai dai akwai alamu da ke nuna cewa wannan rana ko mai bi mata za su kasance ranakun hutun ma’aikata.

“Haka kuma mu na sane da cewa wasu da su ka yi rajista ta yanar gizo sun sanya ranar kammala rajistar su a waɗannan ranaku da za su iya zama na hutun ma’aikata.

“Hukumar za ta yi taro a ranar Alhamis ta wannan makon domin yin nazari kan lamarin saboda a samu matsaya a kan shi.”

Ya ce jadawalin lokutan na tsawon zango huɗu na shekara ne, kuma a zangon farko za a yi rajistar masu zaɓe daga ranar 28 ga Yuni zuwa 1 ga Satumba, yayin da za a kafe sunayen masu rajistar daga 4 ga Satumba zuwa 30 ga Satumba.

Zango na biyu, inji shi, zai fara daga 4 ga Oktoba ya ƙare 20 ga Disamba inda a za a yi rajistar masu zaɓe, yayin da za a kafe sunayen masu rajista daga 24 ga Disamba zuwa 30 ga Disamba.

Ya ƙara da cewa a zango na uku za a yi rajistar masu zaɓe ne daga 3 ga Janairu 3, 2022 zuwa 22 ga Maris, 2022; yayin da za a kafe sunayen masu rajistar saboda ƙorafi ko koke, wanda za a yi daga 26 ga Maris, 2022 zuwa 1 ga Afrilu, 2022.

“Mu na aiki tuƙuru don tabbatar da cewa kamar yadda mu ka fara aikin matakin farko na rajista ta hanyar yanar gizo sumul ƙalau, shi ma fara aikin rajista na ido da ido za a yi shi ba tare da wata matsala ba.”

Tags: AbujaHausaINECLabaraiNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Majalisar Dattawa ta yi biris da koken waɗanda su ka raina kashi 3% ta rattaba hannu kan Dokar Rabon Arzikin Mai ta PIB

Next Post

HIMMA DAI MATA MANOMA: Yadda noman masara, waken soya da kashu ya karɓi matar da ta watsar da aikin banki

Next Post
HIMMA DAI MATA MANOMA: Yadda noman masara, waken soya da kashu ya karɓi matar da ta watsar da aikin banki

HIMMA DAI MATA MANOMA: Yadda noman masara, waken soya da kashu ya karɓi matar da ta watsar da aikin banki

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya
  • Gwamnatin Buhari ta ƙakaba sabbin harajin kira na wayar hannu ga ƴan Najeriya
  • BALA’IN ‘YAN BINDIGA: Sama da Katsinawa 13,000 su ka tsallake ba shiri zuwa Jamhuriyyar Nijar -Gwamna Masari
  • TAKARAR SHUGABAN ƘASA 2023: Mutum biyar kaɗai ke da gaske a cikin APC, sauran ‘yan rakiyar amarya ne -Gwamna Fayemi
  • Babu wanda na ke bibiya yayi min mataimakin shugaban kasa – Zulum

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.