• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari Travelling

    Duk da tsananin hare-haren da ya darkaki Najeriya a kwanakin nan Buhari zai waske taro Dakar

    An cika sansani uku fal da tubabbun ‘yan Boko Haram -Gwamna Zulum

    An cika sansani uku fal da tubabbun ‘yan Boko Haram -Gwamna Zulum

    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari Travelling

    Duk da tsananin hare-haren da ya darkaki Najeriya a kwanakin nan Buhari zai waske taro Dakar

    An cika sansani uku fal da tubabbun ‘yan Boko Haram -Gwamna Zulum

    An cika sansani uku fal da tubabbun ‘yan Boko Haram -Gwamna Zulum

    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Minista Lai Mohammed ya lailaya ƙarya, bai ɗauki nauyin kamfen ɗin mu ba -‘Yan Majalisar Dokokin Kwara

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
July 5, 2021
in Labarai
0
Gwamnan Kwara ya ci amana ta bayan ni kaɗai na kashe masa dukkan kuɗaɗen da ya ci zaɓen 2019 – Lai Mohammed

Ƴan Majalisar Dokin Jihar Kwara na APC su 21, sun ƙaryata iƙirarin da Ministan Yaɗa Labarai, Lai Mohammed ya yi, inda ya ce shi ya ɗauki nauyin biyan kuɗin kamfen ɗin su da kamfen ɗin Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq na Jihar Kwara.

Cikin wani taron manema labarai da su ka kira a ranar Lahadi a Ilorin, su 21 ɗin sun ce ƙarya Lai ya ke yi.

“Duk abin da mu ka kashe wajen kamfen da fosta da sauran hidindimun zabe, duk Gwamna ya ba mu, a lokacin shi ma ya na takara.

“Sai fa Hedkwatar APC ta Ƙasa da ta bai wa kowanen mu naira 500,000. Amma Minista Lai ko sisi bai ba kowa ba.

“To ina Lai ya ke da jama’a ko da a ƙaramar hukumar sa ta haihuwa da har za su amince masa su ɗauki maƙudan kuɗaɗen da ya ce ya tara ya bai wa gwamna domin kamfen?”

Kalaman Da Su Ka Jawo ‘Yan Majalisar Dokokin Kwara Watsa Wa Minista Lai Mohammed Kasa A Ido:

“Gwamnan Kwara ya ci amana ta bayan ni kaɗai na kashe masa dukkan kuɗaɗen da ya ci zaɓen 2019”

Dambarwa da karankatakaliyar rikici na ci gaba da ƙara muni tsakanin Gwamnan Kwara AbdulRazaq AbdulRahman da Ministan Yaɗa Labarai, Lai Mohammed, shekaru biyu bayan sun yi taron dangin ‘O to ge’ sun ruguza gidan siyasar Bukola Saraki a jihar Kwara.

Lai Mohammed ya bayyana cewa shi ya ɗauki nauyin takarar da Gwamna AbdulRahman ya ci zaɓen 2019, amma kuma yanzu ya zo ya ci amanar sa.

Yadda Na Ɗauki Nauyin Takarar Gwamnan Kwara -Lai Mohammed

“Bari na faɗa maku, ba don ni ba da AbdulRahman bai ci kujerar Gwamnan Kwara ba. Ni kaɗai na tara masa dukkan kuɗaɗen da aka yi masa kamfen da waɗanda shi ma ya yi kamfen da su.

“Mutumin da ba shi da ko ranyo, ni na riƙa bin abokai na, abokan siyasa ta, abokan arziki, ‘yan siyasa da ‘yan uwa na kusa da na nesa ina tara kuɗaɗen da Gwamna AbdulRahman ya yi kamfen.

“Ina ƙalubalantar duk wani wanda ya ba shi ko ya tara masa kuɗi ko nawa ne, ya fito ya ƙaryata ni.

“Ni na biya kuɗaɗen da aka ejan-ejan na jam’iyya da shugabannin jam’iyya a matakai daban-daban domin su tattaro mana masu jefa ƙuri’a.

Gudummawar Babura 500 Na Bayar Da Motoci 20 Don AbdulRahman Ya Ci Zaɓen 2019 -Lai Mohammed

Minista Lai ya ce, “hatta babura 500 da motoci 20 waɗanda aka raba, duk ni na bayar da su.”

“Haka na bayar da kuɗin kamfen naira miliyan 100 ga Ɗan Majalisar Tarayya Tunji Ajuloopin, amma ya dagargaje naira miliyan 70, aka nema aka rasa, sai naira miliyan 30 kaɗai ya yi kamfen da su. Kuma zaɓen na sa ne ba nawa ba.”

Sai Da Aka Ce Min AbdulRahman Kara Da Kiyashi Ne -Lai Mohammed

Lai ya nuna rashin jin daɗin duk wannan ƙoƙarin da ya yi wa Gwamnan Kwara, amma kuma tun tafiya ba ta yi nisa ba, ya ci amana ta.

Ya ce tun farko da wasu masu kaifin tunani su ka ya tattago AbdulRahman Abdulrazaq, an ba shi shawara cewa ya rabu da shi, domin kara da kiyashi ne, amma bai karɓi shawarar ba.

Da ya koma kan batun ‘yan jam’iyya waɗanda ba a yi wa rajista ba kuwa, Lai ya ce Shugaban Riƙon Jam’iyyar APC, Mai Mala Buni ya tabbatar masa cewa kafin a yi gangamin jam’iyya na Jihar Kwara, sai an fara yin cikakken aikin rajistar ‘ya’yan jam’iyyar waɗanda ba a yi wa rajista ba.

PREMIUM TIMES Hausa ta buga cikakkiyar salsalar rikicin na su wanda ya samo asali sanadiyyar ƙin sabunta rajistar ‘yan APC na Jihar Kwara magoya bayan Lai Mohammed da sauran ‘yan ɓangaren sa.

Jaridar ta bada cikakken labarin yadda gaggan da su ka ruguza gidan siyasar Bukola Saraki sun fara ƙwaƙule wa junan su idanu a Kwara.

Shekaru biyu tun ba a yi nisa da yin amfani da salon kamfen ɗin ‘O to ge’ aka ruguza gidan siyasar tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, daga sama har ƙasa a Jihar Kwara, tun ba a yi nisa ba har gayyar ta watse, zaratan da su ka ga bayan Saraki sun juya su na yaƙar junan su da makaman da su ka yaƙi Saraki da su.

Gidan Siyasar Saraki dai ya kafu ne tun zamanin tsohon Shugaban Majalisar Dattawa na zamanin Jamhuriya ta Biyu, Olusola Saraki, mahaifin Bukola da Gbemisola Saraki.

Bayan Bukola Saraki ya yi Gwamna shekaru takwas, ya ɗora Abdulfatah Ahmed, wanda ya yi shekaru huɗu na farko a ƙarƙashin PDP.

Bayan kafa nPDP, ya bi Saraki sun koma APC, inda a can ma ya sake lashe zaɓe ya shekara huɗu.

To sai dai kuma gangamin ‘O to ge’ a lokacin zaɓen 2019 da aka yi domin kawo ƙarshen siyasar gidan Saraki, ya yi nasara.

Nasarar farko dai wanda APC ta tsaida takarar gwamna a Kwara shi ya yi nasara, wato AbdulRahman Abdulrazaq.

Nasara ta biyu kuma Saraki da duk waɗanda su ka fito takara a ƙarƙashin tutar sa sun ci ƙasa ba su yi nasara ba.

Gungun Ruguza Gidan Siyasar Saraki:

Wannan gungu sun haɗa da ‘Legacy Group’, wanda ya ƙunshi Gbemisola Saraki, ƙanwar Bukola Saraki, wadda ba su ga-maciji. Ita ce bayan nasarar zaɓen 2019 aka naɗa ta Ƙaramar Ministar Sufuri.

Akwai kuma gungun AA Group, wato Gwamna a yanzu wanda shi gungun mayaƙan su ka tsayar takarar gwamna, kuma ya yi nasara.

Akwai irin su Ministan Yaɗa Labarai, Lai Mohammed, wasu ɗaiɗaiku irin shugaban jam’iyyar a APC na lokacin, Bashir Bolarinwa.

Yadda Aka Fara Kitso Da Kwarkwata A Cikin Kai:

Tun a wurin zaɓen fidda gwani aka fara samun tangarɗa, inda a bisa kuskure aka soke ‘yan takara biyu, Salihu Mustapha da Mashood Mustapha.

Sai da ta kai uwar jam’iyyar APC ta ƙasa sun ba su haƙuri dangane da abin da aka yi masu. Duk da wasu na ganin cewa tuggu ne aka ƙulla masu, amma dai sun haƙura ba su kai ƙara ba.

Dawowa Rakiyar Gwamna Watanni Shida Bayan Zaɓe:

An shafe watanni shida kafin Gwamnan Kwara A.A ya naɗa kwamiahinoni. Hakan kuwa ya ɓata wa da dama gaggan APC na Kwara rai.

An samu saɓani da cukumurɗar tuggu da kutunguilar siyasa, har ta kai an tsige Shugaban Jam’iyya Bashir Bolarinwa. An yi zargin da hannun Gwamna aka kori Bolarinwa daga shugabancin APC a Kwara.

Shugaban Kwamitin Riƙon APC, Mai Mala-Buni ya naɗa Abdullahi Samari shugabancin rikon APC a Kwara bayan tsige Bolarinwa.

Tsige naɗa Borarinwa da naɗa Abdullahi Samari, ya fasa jam’iyyar APC gida biyu a Jihar Kwara. Akwai masu goyon bayan Gwamna, akwai kuma waɗanda ba su goyon bayan sa.

Rigimar Gwamna Da Minista Lai Mohammed:

Alaƙa ta yi tsami tsakanin Gwamna da Minista Lai Mohammed a lokacin sabunta rajistar ‘ya’yan jam’iyyar APC, inda Lai Mohammed ya ce “iya-shege” aka yi ba sabunta rajista ba.

PREMIUM TIMES HAUSA ta bada labarin yadda Gwamnan Kwara ya tashi da katinan rajistar ‘yan jam’iyya sama, ya bar Lai Mohammed ya na susar ƙeya.”

Minista Lai a lokacin ya kira taron manema labarai a garin su Oro, inda ya nemi a sake sabunta rajista a jihar Kwara, domin Gwamna ya kwashe katin rajista ya raba wa magoya bayan sa.

Lai ya yi zargin cewa ba a bi tsarin da jam’iyyar APC ta gindaya wajen sabunta rajista ba.

Wakilin mu ya tabbatar da wani zargi da Lai Mohammed ya yi, inda ya ce ba a yi amfani da littafin rajistar mambobi ba, sai aka yi amfani da fallayen takardu, waɗanda hatta shi kan sa gwamnan ma da mutanen sa duk a fallayen farar takarda aka yi rajistar sunayen su.

Tuni dai wannan gayya ta watse kowa ya kama gaban sa. Jama’a da dama na ganin idan Saraki ya sake yunƙurawa a zaɓen 2023, zai dawo da martabar gidan siyasar Saraki daram.

Tags: AbujaLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Ma’aikatar Jinƙai za ta shigar da ƙarin yara miliyan 5 a shirin ciyar da ƴan makaranta kafin 2023 -Minista Sadiya

Next Post

Yawan yaran makaranta da gwamnati ke ciyarwa a jihar Kano ya haura miliyan 2 – Gwamnatin Kano

Next Post
Yawan yaran makaranta da gwamnati ke ciyarwa a jihar Kano ya haura miliyan 2 – Gwamnatin Kano

Yawan yaran makaranta da gwamnati ke ciyarwa a jihar Kano ya haura miliyan 2 - Gwamnatin Kano

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • KOWA TA SA TA FISSHE SHI: Ƙoƙarin haɗewar LP da NNPP ya kakare, Peter Obi zai bayyana mataimakin takarar sa ranar Juma’a
  • ‘Da gangar aka bari ƴan bindiga suka kai harin gidan yarin Kuje, saboda na yi ta faɗin hakan zai auku – Mamu
  • Ƴan bindiga sun babbake cibiyoyin kiwon lafiya sun yi dalilin dole aka rufe wasu 69 a Katsina
  • Dala ta ƙara kekketa wa naira rigar mutunci daidai lokacin tsadar kayan abinci
  • Duk da tsananin hare-haren da ya darkaki Najeriya a kwanakin nan Buhari zai waske taro Dakar

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.