• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kwara ya ci amana ta bayan ni kaɗai na kashe masa dukkan kuɗaɗen da ya ci zaɓen 2019 – Lai Mohammed

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
July 4, 2021
in Babban Labari, Rahotanni
0
Gwamnan Kwara ya ci amana ta bayan ni kaɗai na kashe masa dukkan kuɗaɗen da ya ci zaɓen 2019 – Lai Mohammed

Dambarwa da karankatakaliyar rikici na ci gaba da ƙara muni tsakanin Gwamnan Kwara AbdulRazaq AbdulRahman da Ministan Yaɗa Labarai, Lai Mohammed, shekaru biyu bayan sun yi taron dangin ‘O to ge’ sun ruguza gidan siyasar Bukola Saraki a jihar Kwara.

Lai Mohammed ya bayyana cewa shi ya ɗauki nauyin takarar da Gwamna AbdulRahman ya ci zaɓen 2019, amma kuma yanzu ya zo ya ci amanar sa.

Yadda Na Ɗauki Nauyin Takarar Gwamnan Kwara -Lai Mohammed

“Bari na faɗa maku, ba don ni ba da AbdulRahman bai ci kujerar Gwamnan Kwara ba. Ni kaɗai na tara masa dukkan kuɗaɗen da aka yi masa kamfen da waɗanda shi ma ya yi kamfen da su.

“Mutumin da ba shi da ko ranyo, ni na riƙa bin abokai na, abokan siyasa, abokan arziki, ƴan siyasa da ‘yan uwa na kusa da na nesa ina tara kuɗaɗen da Gwamna AbdulRahman ya yi kamfen.

“Ina ƙalubalantar duk wani wanda ya ba shi ko ya tara masa kuɗi ko nawa ne, ya fito ya ƙaryata ni.

“Ni na biya kuɗaɗen da aka ejan-ejan na jam’iyya da shugabannin jam’iyya a matakai daban-daban domin su tattaro mana masu jefa ƙuri’a.

Gudummawar Babura 500 Na Bayar Da Motoci 20 Don AbdulRahman Ya Ci Zaɓen 2019 -Lai Mohammed

Minista Lai ya ce, “hatta babura 500 da motoci 20 waɗanda aka raba, duk ni na bayar da su.”

“Haka na bayar da kuɗin kamfen naira miliyan 100 ga Ɗan Majalisar Tarayya Tunji Ajuloopin, amma ya dagargaje naira miliyan 70, aka nema aka rasa, sai naira miliyan 30 kaɗai ya yi kamfen da su. Kuma zaɓen na sa ne ba nawa ba.”

Sai Da Aka Ce Min AbdulRahman Kara Da Kiyashi Ne -Lai Mohammed

Lai ya nuna rashin jin daɗin duk wannan ƙoƙarin da ya yi wa Gwamnan Kwara, amma kuma tun tafiya ba ta yi nisa ba, ya ci amana ta.

Ya ce tun farko da wasu masu kaifin tunani su ka ya tattago AbdulRahman Abdulrazaq, an ba shi shawara cewa ya rabu da shi, domin kara da kiyashi ne, amma bai karɓi shawarar ba.

Da ya koma kan batun ‘yan jam’iyya waɗanda ba a yi wa rajista ba kuwa, Lai ya ce Shugaban Riƙon Jam’iyyar APC, Mai Mala Buni ya tabbatar masa cewa kafin a yi gangamin jam’iyya na Jihar Kwara, sai an fara yin cikakken aikin rajistar ‘ya’yan jam’iyyar waɗanda ba a yi wa rajista ba.

PREMIUM TIMES Hausa ta buga cikakkiyar salsalar rikicin na su wanda ya samo asali sanadiyyar ƙin sabunta rajistar ‘yan APC na Jihar Kwara magoya bayan Lai Mohammed da sauran ‘yan ɓangaren sa.

Jaridar ta bada cikakken labarin yadda gaggan da su ka ruguza gidan siyasar Bukola Saraki sun fara ƙwaƙule wa junan su idanu a Kwara.

Shekaru biyu tun ba a yi nisa da yin amfani da salon kamfen ɗin ‘O to ge’ aka ruguza gidan siyasar tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, daga sama har ƙasa a Jihar Kwara, tun ba a yi nisa ba har gayyar ta watse, zaratan da su ka ga bayan Saraki sun juya su na yaƙar junan su da makaman da su ka yaƙi Saraki da su.

Gidan Siyasar Saraki dai ya kafu ne tun zamanin tsohon Shugaban Majalisar Dattawa na zamanin Jamhuriya ta Biyu, Olusola Saraki, mahaifin Bukola da Gbemisola Saraki.

Bayan Bukola Saraki ya yi Gwamna shekaru takwas, ya ɗora Abdulfatah Ahmed, wanda ya yi shekaru huɗu na farko a ƙarƙashin PDP.

Bayan kafa nPDP, ya bi Saraki sun koma APC, inda a can ma ya sake lashe zaɓe ya shekara huɗu.

To sai dai kuma gangamin ‘O to ge’ a lokacin zaɓen 2019 da aka yi domin kawo ƙarshen siyasar gidan Saraki, ya yi nasara.

Nasarar farko dai wanda APC ta tsaida takarar gwamna a Kwara shi ya yi nasara, wato AbdulRahman Abdulrazaq.

Nasara ta biyu kuma Saraki da duk waɗanda su ka fito takara a ƙarƙashin tutar sa sun ci ƙasa ba su yi nasara ba.

Gungun Ruguza Gidan Siyasar Saraki:

Wannan gungu sun haɗa da ‘Legacy Group’, wanda ya ƙunshi Gbemisola Saraki, ƙanwar Bukola Saraki, wadda ba su ga-maciji. Ita ce bayan nasarar zaɓen 2019 aka naɗa ta Ƙaramar Ministar Sufuri.

Akwai kuma gungun AA Group, wato Gwamna a yanzu wanda shi gungun mayaƙan su ka tsayar takarar gwamna, kuma ya yi nasara.

Akwai irin su Ministan Yaɗa Labarai, Lai Mohammed, wasu ɗaiɗaiku irin shugaban jam’iyyar a APC na lokacin, Bashir Bolarinwa.

Yadda Aka Fara Kitso Da Kwarkwata A Cikin Kai:

Tun a wurin zaɓen fidda gwani aka fara samun tangarɗa, inda a bisa kuskure aka soke ‘yan takara biyu, Salihu Mustapha da Mashood Mustapha.

Sai da ta kai uwar jam’iyyar APC ta ƙasa sun ba su haƙuri dangane da abin da aka yi masu. Duk da wasu na ganin cewa tuggu ne aka ƙulla masu, amma dai sun haƙura ba su kai ƙara ba.

Dawowa Rakiyar Gwamna Watanni Shida Bayan Zaɓe:

An shafe watanni shida kafin Gwamnan Kwara A.A ya naɗa kwamiahinoni. Hakan kuwa ya ɓata wa da dama gaggan APC na Kwara rai.

An samu saɓani da cukumurɗar tuggu da kutunguilar siyasa, har ta kai an tsige Shugaban Jam’iyya Bashir Bolarinwa. An yi zargin da hannun Gwamna aka kori Bolarinwa daga shugabancin APC a Kwara.

Shugaban Kwamitin Riƙon APC, Mai Mala-Buni ya naɗa Abdullahi Samari shugabancin rikon APC a Kwara bayan tsige Bolarinwa.

Tsige naɗa Borarinwa da naɗa Abdullahi Samari, ya fasa jam’iyyar APC gida biyu a Jihar Kwara. Akwai masu goyon bayan Gwamna, akwai kuma waɗanda ba su goyon bayan sa.

Rigimar Gwamna Da Minista Lai Mohammed:

Alaƙa ta yi tsami tsakanin Gwamna da Minista Lai Mohammed a lokacin sabunta rajistar ‘ya’yan jam’iyyar APC, inda Lai Mohammed ya ce “iya-shege” aka yi ba sabunta rajista ba.

PREMIUM TIMES HAUSA ta bada labarin yadda Gwamnan Kwara ya tashi da katinan rajistar ‘yan jam’iyya sama, ya bar Lai Mohammed ya na susar ƙeya.”

Minista Lai a lokacin ya kira taron manema labarai a garin su Oro, inda ya nemi a sake sabunta rajista a jihar Kwara, domin Gwamna ya kwashe katin rajista ya raba wa magoya bayan sa.

Lai ya yi zargin cewa ba a bi tsarin da jam’iyyar APC ta gindaya wajen sabunta rajista ba.

Wakilin mu ya tabbatar da wani zargi da Lai Mohammed ya yi, inda ya ce ba a yi amfani da littafin rajistar mambobi ba, sai aka yi amfani da fallayen takardu, waɗanda hatta shi kan sa gwamnan ma da mutanen sa duk a fallayen farar takarda aka yi rajistar sunayen su.

Tuni dai wannan gayya ta watse kowa ya kama gaban sa. Jama’a da dama na ganin idan Saraki ya sake yunƙurawa a zaɓen 2023, zai dawo da martabar gidan siyasar Saraki daram.

Tags: abdulrqzaqAbujaKwaraLabaraiLaiMohammedNews
Previous Post

KANO: KAROTA ta maida lasisin tuƙa Keke NAPEP Naira 100,000 daga naira 8,000

Next Post

Za a maida duk baƙon da ya shigo Najeriya ba tare da shaidar gwajin korona ba – Gargaɗin Gwamnati

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
An bude filin jirgin saman Abuja cikin tsarin kare fasinjoji daga kamuwa da yada Korona

Za a maida duk baƙon da ya shigo Najeriya ba tare da shaidar gwajin korona ba - Gargaɗin Gwamnati

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Kada ku tausaya min don na faɗi zaɓen Sanatan Zamfara – Sanata Marafa
  • JIRAN TSAMMANI: Tinubu zai saka wa waɗanda su ka yi wa APC hidima da waɗanda su ka wahala saboda jam’iyya – Marafa
  • Uba Sani ya yi sabbin nade-nade 27, ya nada Sani Liman shugaban ma’aikatan fadar gwamnati
  • SHUGABANCIN MAJALISAR DATTAWA: ‘A saka min wahalar da na yi wa APC, a ba ni shugabancin Majalisar Dattawa’ – Osita Izunaso
  • SHUGABANCIN MAJALISA: ‘Ba zan janye wa kowa ba, amma na ‘jone’ da guruf ɗin Abdul’aziz Yari’ – Orji Kalu

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.