Shugaba Muhammadu Buhari ya gargaɗi ‘yan kasuwa, ‘yan kwangila da sauran manyan Najeriya masu ƙumbar susa su guji ƙoƙarin yi masa kyauta ko shi ko jami’an gwamnatin sa.
Da ya ke jawabi a Fadar Sarkin Daura, lokacin da ya je gaisuwar fada, Buhari ya ce, “ba na buƙatar kuɗin ku. Ku ɗauki kuɗin ku yi wa je ku taimaki jama’a mabuƙata da su, maimakon su riƙa bai wa ma’aikatan sa na ofis ko jami’an gwamnatin sa kuɗaɗe.
Buhari ya kai gaisuwar fada tare da ɗan sa Yusuf Buhari, wanda aka naɗa Talban Daura’ sai kuma Musa Daura da aka naɗa Danmadamin Daura.
“Ba mu buƙatar kuɗaɗe daga wani mutum ko wata ƙungiya a matsayin ladar wani aiki ko kwangilar da aka ba shi. Su tuna akwai ayyukan inganta rayuwar al’ummar da za su iya yi da kuɗaɗen.” Inji Buhari.
Buhari ƙara da cewa ya na so ya riƙa kai ziyara Daura akai-akai, amma saboda tsadar kuɗaɗen da ake kashewa wajen zirga-zirgar tafiye-tafiyen Shugaban Ƙasa da kuma karakainar kai jami’an tsaro cikin yanayin da ba su saba ya, shi ya sa ya ke taƙaita yawan zuwan.
“Kowa ya san mu da noma, domin Ni ma ina da gona a nan Daura. Zan so na riƙa zuwa duk bayan mako biyu, kuma ba wanda zai hana ni zuwa. Amma gara a riƙa kashe kuɗaɗen jama’a ana gina wa yaran su makarantu da asibitoci da a riƙa kashe kuɗaɗen wajen karakainar zuwa na ganin gida.”
Sarkin Daura ya ce zuwa ganin gida da Buhari ke yi, ya nuna matuƙar kyawawan halaye da ɗabi’un sa.
Discussion about this post