Shari’ar da aka shafe shekaru tara ana tuhumar tsohon Dan Majalisar Tarayya, Farouk Lawan da laifin karɓar toshiyar bakin dala 500,000 daga hannun hamshaƙin attajiri kuma babban dillalin fetur, ta zo ƙarshe, domin an ɗaure shi shekaru bakwai a kurkuku.
A yau Talata ne aka yanke wa Lawan hukunci a ƙarƙashin Babban Kotun Babban Birnin Tarayya da ke Abuja. To sai dai kuma yayin da wanda ake tuhuma ya tsaya kai da fata cewa bai karɓi cin hancin ba, Mai Shari’a Angela Otaluka ta yi watsi da roƙon da Lawan ya yi.
Ana tuhumar Lawan da laifin karɓar toshiyar bakin dala 500,000 daga hannun Femi Otedola a bisa yarjejeniyar cewa za a cire sunan kamfanin sa daga cikin kamfanonin da Kwamitin Majalisa Mai Binciken Harƙallar Kuɗaɗen Tallafin Fetur, ya kama da laifi dumu-dumu.
Lawan an zarge shi da laifin neman cin hancin dala miliyan 3, a madadin shi Shugaban Kwamiti da kuma sauran mambobin kwamiti.
Otedola ya shaida wa duniya cewa ya ɗana wa Lawan tarko, kuma ya kama shi, domin kyamara ta nuno lokacin da ake ba shi kuɗaɗen, haka an nuno lokacin da ya ke karɓar.
Otedola ya ce ya fara ba shi dala 500,000 ce, saura dala miliyan 2.5 kenan.
An maka kotu tun cikin 2012, inda aka shafe shekaru tara kenan, ana ƙaƙudubar shari’a.
Bayan shari’a ta yi nisa, Lawan ya garzaya Babbar Kotun Tarayya ta Abuja, inda ya nemi kotun ta dakatar da Babbar Kotun Abuja, domin a cewar sa bai karɓi toshiyar bakin ba.
Kotun dai ta ce ya na da tuhumar da zai amsa, don haka a je a ci gaba da shari’a.
An shirya zartas da hukunci a kan sa tun cikin makon da ya gabata. Amma haka bai yiwu ba, sai Mai Shari’a ta tsaida ranar yau Talata.
Yayin da aka zauna yau Talata, Mai Shari’a ta share fagen yanke masa hukunci, yayin da ta ƙi karɓar uzurin sa cewa bai aikata laifin da ake tuhumar sa ba.
Kafin Mai Shari’a Otaluka dai alƙalai biyu sun saurari ƙarar a shekarun baya. Na farko ƙarin girma aka yi masa zuwa Babbar Kotun Tarayya.
Mai Shari’a ta biyu kuma janye hannun ta ta yi a shari’ar, saboda Lawan ya zarge ta da nuna masa bambanci da rashin adalci.