Sanata Peter Owaoboshi, wanda aka fi zarga da tafka babbar gurungunɗumar harƙalla a Hukumar Raya Yankin Neja Delta (NDDC), ya sauya sheƙa zuwa APC, inda ya samu kyakkyawar tarba daga Shugaba Muhammadu Buhari.
Cikin watan Yuli ne dai NDDC ta zargi Nwaoboshi da harƙallar kwangiloli na naira biliyan 3.6.
An zarge shi da laifin yin amfani da sunayen kamfanoni 11 ya samar wa kan sa kwangiloli a NDDC, alhali kuma shi ne Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da NNDC ɗin da kuma Harkokin Neja Delta.
Nwaoboshi ya koma jam’iyyar APC, inda yau Juma’a Shugaba Buhari ya yi masa murnar komawa jam’iyyar mutane masu kawo sauyin ci gaban al’umma, wato APC.
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ovie Omo-Agege ne ya yi masa iso ga Buhari.
An dai zargi sanata da harƙallar kwangilolin da har Kakakin Yaɗa Labarai na Hukumar NDDC, Charles Odili ya shaida wa PREMIUM TIMES cewa ba a taɓa yin harƙallar da ta fara muni a NDDC ba, kamar ta Nwaoboshi.
Idan ba a manta ba, Ministan Harkokin Neja Delta, Godswill Akpabio, ya fallasa cewa da haɗin bakin ‘yan majalisa ake harƙalla a Hukumar Neja Delta.
Ya buga misali da cewa akwai lokacin da aka karkatar da dala miliyan 70 ta daɗe ajiye a wani banki.
Owaoboshi dai ya ƙaryata zargin da ake yi masa. Kuma har yau duk da ɗaukar hankali da Kwamitin Binciken Harƙallar NDDC ya yi cikin 2020, a Majalisa, har yau ba a lama kowa ba, kuma ba a hukunta kowa na.
Wanda aka fi zargin ma ga shi ya koma APC mai mulki, daga jam’iyyar PDP.