Jam’iyyar PDP ta gargaɗi Gwamna Bello Matawalle na Jihar Zamfara cewa idan ya koma APC zai rasa kujerar sa ta gwamna sukutum.
A cikin wata ganawa da ya yi da manema labarai a Abuja, Kakakin Jam’iyyar PDP, Kola Ologbondiyan ya jaddada wa Matawalle cewa PDP ta ci zaɓen Gwamnan Zamfara ne da ƙuri’u, kuma Kotun Ƙoli ce ta tabbatar masa da kujerar.
Saboda haka ya ce tunda INEC ta haramta wa APC muƙaman gwamna, na mataimaki, sanatoci da na ‘yan majalisar tarayya, kuma Kotun Koli ta tabbatar, don haka doka ta haramta wa APC yin mulki a jihar Zamfara kenan, tsakanin 2019 zuwa 2023.
Haka kuma PDP ta gargaɗi ‘yan Majalisar Dattawa da na Tarayya na Jihar Zamfara har ma da na Majalisar Dokoki na jiha cewa kada su bari a ribbace su har su rasa kujerun su.
“Saboda dokar ƙasa dai ta ce ‘yan majalisa ba za su canja sheƙa daga wannan jam’iyya zuwa waccan ba, har sai idan akwai rikici na cikin gida a cikin jam’iyyar su.
“Kasassaɓar da Bello Matawalle ke son yi ganganci ne ƙarara, domin zai burma wa cikin sa wuƙa ne kawai. Saboda dokar INEC da kuma Kotun Koli duk sun haramta wa APC yin mulki a jihar Zamfara, saboda kwata-kwata ba su cikin ‘yan takara.”
APC dai ba ta cikin jam’iyyun takara a Zamfara, saboda ta
ba a yi zaɓen fidda-gwani bisa ƙa’ida ba. A kan haka ne INEC da Kotun Koli su ka hana su takara.