• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari Travelling

    Duk da tsananin hare-haren da ya darkaki Najeriya a kwanakin nan Buhari zai waske taro Dakar

    An cika sansani uku fal da tubabbun ‘yan Boko Haram -Gwamna Zulum

    An cika sansani uku fal da tubabbun ‘yan Boko Haram -Gwamna Zulum

    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari Travelling

    Duk da tsananin hare-haren da ya darkaki Najeriya a kwanakin nan Buhari zai waske taro Dakar

    An cika sansani uku fal da tubabbun ‘yan Boko Haram -Gwamna Zulum

    An cika sansani uku fal da tubabbun ‘yan Boko Haram -Gwamna Zulum

    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

ALLURA CIKIN RUWA: Wa APC Za Ta Zaba Don Zama Shugaban Jam’iyya A Katsina? Daga Muhammad Bello

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
June 7, 2021
in Rahotanni
0
ALLURA CIKIN RUWA: Wa APC Za Ta Zaba Don Zama Shugaban Jam’iyya A Katsina? Daga Muhammad Bello

Ganin watanni shida da uwar jam’iyyar APC ta tsara domin shirya taron jam’iyyar da za’a zabi shugabannin a kowane matakai ya na ƙara matsowa, kusan saura kwanaki ƙalilan. An fara hasashen su wa za su zama shugabannin jam’iyar a matakan ƙasa da jihohi da shiyyoyi da ƙananan hukumomi da kuma gundumomi a duk faɗin ƙasa.

Duk da wasu na ganin kwamitin riƙon na ƙasa bai shirya gudanar da wannan taron ƙasa ba, wasu ma har sun fara yamaɗiɗin cewa shugabancin na Gwamna Mai Mala Buni za su ƙara neman wa’adin, kamar zuwa yanzu ba su shirya gudanar da zaben ba. Saboda zuwa yanzu ya kamata a ce sun fitar da yadda jaddawalin zabe da kuma sharuɗɗan tsayawa takara a matakai daban-daban.

A Jihar Katsina ma an fara hasashen waɗanda za su tsaya takarar muƙamai sama da ashirin da za’a cike guraben su. Wasu daga cikin masu son sha’awar tsayawa wa takara sun fara tuntuba ta ƙarƙashin ƙasa, wasu kuma suna tuntubar iyayen gidan su yadda za’a bullo wa tsayawa takarar muƙamai daban-daban. Abin da mutanen Jihar Katsina ke tambaya shi ne, shin Gwamna ko Gwamnatin Jiha na da wanda ta tsaida? Shin za’a yi karba-karba tsakanin shiyyoyin Katsina da Daura da kuma Funtua saboda yanzu ɗan shiyyar Katsina ke yi? Mataimakin Gwamna Mannir Yakubu da Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, ana kallon kamar su na da sha’awar tsayawa takarar gwamna.

Shin kowane daga cikin su zai tsaida ɗan takara?

Aƙalla wakilan jamiyyar 4,814 daga matakai daban-daban ne ake sa ran za su jefa ƙuri’a a matakin shugabancin jam’iyyar APC a Jihar Katsina. Akwai muƙamai a matakin jiha har guda 20, waɗanda za’a zaba, domin tafiyar da jamiyyar a matakin jiha.

Kamar yadda kowa ya sani, uwar jam’iyyar APC a matakin ƙasa ta rushe kafatanin shugabancin jam’iyyar a matakan ƙasa da jihohi da ƙananan hukumomi a duk faɗin ƙasar nan.

Wannan ya bai wa Shugaban Jam’iyyar a Jihar Katsina, Malam Shitu S. Shitu damar ci gaba da tafiyar da jam’iyyar tare da kwamitin zartaswa na jam’iyyar na jiha da na shiyya. Haka kuma Shugaban Rikon jam’iyyar na jiha, Malam Shitu ya rantsar da shugabannin jam’iyyar na rikon a helkwatar jam’iyyar ta jiha a matakin ƙananan hukumomi talatin da huɗu na jihar Katsina su ma su tafi su ci gaba da jan ragamar jam’iyyar, kamar yadda uwar jam’iyyar ta ƙasa ta umurta.

A halin da ake ciki yanzu dai jam’iyyar APC ba ta da zababbun shugabannin jam’iyya a kowane matakai, sai da shugabannin riƙo kafin a fiddo da jaddawalin zaben. A jihar Katsina akwai muƙamai sama da guda 20, wanda tuni wasu daga cikin masu rikon kwaryar jam’iyyar a matakai daban-daban sun fara nuna sha’awar su ta tsayawa takarar shugabancin jam’iyyar APC mai mulki a ƙasar nan dama jihar Katsina, inda nan ne mahaifar Shugaba Muhammadu Buhari.

A jihar Katsina dai, yanzu kallo ya fara komawa sama, watau ga wa zai shugabanci jam’iyyar APC a jihar? Kuma su wa su ka fara nuna sha’awar tsayawa takarar? Shin jam’iyyar APC za ta yi karba-karba ne ganin Gwamna ya fito daga shiyyar Funtua, shi kuma shugaban jam’iyyar ya fito daga shiyyar Katsina? Ko kuwa duk mai sha’awar tsayawa takarar shugabancin ya na iya tsayawa ba tare da la’akari da shiyyar da ya fito ba? Shin ko za a duba yiwuwar inda za’a fitar da dan takarar gwamna a zaben 2023? Me ya sa har yanzu masu sha’awar tsayawa takarar kujeru mabanbanta ba su fito suka fara nuna sha’awar tsayawa ba duk sauran yan kwanaki ƙalilan an gudanar da zaben? Wadannan su ne tambayoyin masu sharhi a kan harkokin siyasa da ma wasu daga cikin ‘yan siyasa jihar Katsina.

Ga wasu mutum biyar, waɗanda ake kyautata zaton ɗaya daga cikin su zai samu zarafin ɗarewa kujerar shugabancin jam’iyyar APC a Jihar Katsina:

MALAM SHITU SHU’AIBU SHITU: Shi ne Shugaban Kwamitin Riko na jam’iyyar APC a Jihar Katsina a halin yanzu. Malam Shitu gogaggen dan siyasa, wanda tun da aka dawo mulkin damakaradiyya a shekarar 1999, bai taba sauya sheka ko ya bi wata jami’yya mai mulki ba, jam’iyyar adawa aka san shi ta shugaban kasa muhammadu Buhari har aka kai ga yin nasara a shekarar 2015.

Malam Shitu S. Shitu a zaben shugabannin jam’iyyar APC ta gudanar bayan dunkulewar jam’iyyu wato Maja a shekarar 2014, ya zama jami’in hulda da jama’a da yan jaridu na jamiyyar APC na jihar Katsina a lokacin da aka zabi Malam Mustapha Muhammad Inuwa a matsayin shugabantan na jiha. Bayan samun nasarar zabe da jam’iyyar APC ta samu a jihar Katsina, sai gwamna Aminu Bello Masari ya nada Malam Mustapha Inuwa, sakataren gwamnatin jihar Katsina, inda aka samu gurbi na shugabancin jam’iyyar a lokacin. Sai aka dauko mukkadashin shugaban jam’iyyar na jiha, Abdulkadir Mamman Nasir da ya fito daga shiyya daya da gwamna Masari daga baya aka ba shi Mamman Nasir mukamin mai baiwa gwamna shawara.

Tafiyar Abdulkadir Mamman Nasir ke da wuya aka baiwa jami’in hulda da jama’a da kuma ‘yan jaridu watau (State Public Relation Officer) rikon tafiyar da shugabancin jamiyyar har zuwa a lokacin da aka gudanar da zaben shugabannin jam’iyyar, inda malam Shitu ya zama shugaban jam’iyyar APC mai cikakken iko kuma zababbe.

Malam Shitu S. Shitu kusan shi ne shugaban jam’iyyar APC mafi dade wa kuma shugaban da jam’iyyarsa ke mulkin jihar Katsina da kasar karkashin shugabanci muhammadu Buhari, wanda shima dan asalin jihar Katsina. Haka zalika shugaban rikon na jam’iyyar , an tabbatar yana samu goyan bayan sakataren gwamnatin jihar Katsina, wanda kuma shi ne shugabanta na farko a jihar Katsina.

Malam Shitu yana daya daga cikin wadanda ake ganin zai iya samun nasarar kara darewa bisa wannan kujera ganin cewa dai farko shi ke rike da ita jam’iyyar APC a halin yanzu, na biyu masu sharhi na ganin zai wuyar gaske gwamna Aminu Bello Masari ya juya masa baya ganin irin yadda aka taho a siyasance tare. Na ukku duk wadanda ake hasashen za su yi takarar kusan ya fi su karfin tattalin arzki ko da ace ba zai samu goyan baya daga wasu bangarorin.

Kalubalen da masu sharhi ke ganin zai iya fuskanta na kara darewa kan wannan kujerar, shi ne idan jam’iyyar ta ce za ta duba yiwu war karba-karbar shugabancin a shiyyar Daura da Funtua ko kuma dan takarar gwamna daga wace shiyyar zai fito? Na biyu akwai kalubalen sauran ‘yan takarar gwamnan 2023 da wasu jiga-jigan jam’iyyar da suke ganin ya dauki bangaren takarar Mustapha Inuwa, Sakataren gwamnatin jihar Katsina, wanda ake sa ran zai tsaya takara kuma ga shi amininsa ne, masu sharhi da dama suna ganin wadanan jiga-jigan musamman masu rike da mukaman siyasa a Abuja kuma don son sha’awar tsayawa takara a 2023, za su hada-kai su yaki takarar ta shi.

BALA ABU MUSAWA: Yanzu haka shi ne Mataimakin Shugaban jam’iyyar na shiyyar dan majalisar dattawa na Funtua. Kuma daya daga cikin na hannun-damar gogaggen dan siyasar nan na Najeriya da jihar Katsina, Sanata Abu Ibrahim, wanda an yi ittifakin yaransa ne suka mamaye kafatanin shugabanci jam’iyyar a kowane mataki a yankin Funtua. Ana ganin idan Sanata Abu Ibrahim ya tsayar da Alhaji Bala Abu Musawa, akwai yiwuwar ya samu nasara.

Bala Abu Musawa kuma (Cigarin Musawa)dan siyasa ne da ya ga jiya ya kuma ga yau, kwararre ne wajen iya kalaman jan hankali siyasa, wadanda magoya baya na jin dadin kalaman sa, kusan a halin yanzu yana daga cikin wadanda ake ganin gogewar sa ganin ba shi da tsoro. Amma har zuwa hada wannan rohatan babu wata majiya da ta tabbatar da cewa ya nuna zai tsaya takarar shugabancin jam’iyyar APC a jihar Katsina. Masu sharhi na cewa sau da yawa wajen tarurruka, magoya bayansa na cewa “sai ka yi shugaban jam’iyyar a jihar Katsina’’ an ga yana fara’a da dariya duk lokacin da aka yi masa wannan fatan. Wasu na ganin kamar yana samu goyan bayan mafi rinjayen yan majalisar jiha kuma suna yawan ganawar sirri ta yadda za’a hudo ma samun nasarar cin zaben shugabanci jam’iiyyar. Hatta Matasan yan siyasa suna kallonsa a matsayin wani jigo ko bango sukari duk wanda ya rabe shi sai ya lasa. Farin jinin Bala Abu Musawa ya karade kowacce shiyya, kusan duk cikin mataimakan shugaban jam’iyyar na sauran shiyyar babu mai farin jinin sa a halin yanzu, an yi ittifakin abin hannun shi bai rufe mashi Ido ba ko miskala zarratan, kullum kokarinsa ya samu ya bayar. Mutane na ji dadin faran-faran dinsa da jama’a, da wuya ka ga bacin ransa, yana da kunnuwan sauraren al’umma, ba tare da gajiyawa ba.

Kalubalen da zai iya fuskanta shi ne ubangidan sa, Sanata Abu Ibrahim ya sauka daga sanatan kuma ba shi cikin gwamnati a matakin jiha da na tarayya, amma yana da tsohuwar alaka da jigo a jam’iyyar APC na kasa kuma tsohan gwamnan jihar Legas, Alhaji Bola Ahmad Tinubu. Idan kuma idan har jam’iyyar APC ta tsaida dan takara daga shiyyar Funtua, nan ma zai iya zame ma takarar ta samu tasgaro. Haka zalika, ana ganin sa wajen tarukan Ahmad Dangiwa, Shugaban Banki Bada Lamunin Gidaje Na Kasa da tarukan Shugaban Hukumar Kula Da Kananan Da Matsakaitan Sana’o’I ta kasa Dr. Dikko Radda, ana ganin kamar suna sunsunar tsayawa takarar gwamnan jihar Katsina. Lokaci dai ne kadai zai bayyana sauran dalilan da kalubalen.

SALLAU ARAWA: Dan siyasa ne da ya fito daga kudancin Katsina daga karamar hukumar Dandume a jihar Katsina. Ya taba neman tsayawa takarar mataimakin shugaban jamiyyar na shiyyar Funtua wand abai samu nasara ba, Bala Abu Musawa. Alhaji Sallau Arawa shi ne na hannun damar shugabar Hukumar Kula Da Tashohin Jiragen Ruwa Ta Kasa, Hajia Hadiza Bala Usman. Idan ta goyin bayansa dari bisa dari yay i tasiri sosai a zabe mai zuwa na shugabannin jam’iyyar da yake tafe. Yanzu haka yana shugabantar wata kungiya ta tuntuba dake kananan hukumomi goma sha daya na yanki Funtua, mai rajin kare da zaman jam’iyyar APC day aba tare da tabbatar da hadin kan jam’iyyar APC a shiyyar.

Yanzu babban kalubalen da zai kara fuskanta shi ne yadda fadar shugaban kasa ta dakatar da uwar dakinsa daga shugabanci Hukuma kula da tashoshin jiragen ruwa kuma an kafa kwamitin bincikarta. Zai wahalar gaske har a wanke ta kafin zaben shugabanni jam’iyyar da ake sa ran yi nan gaba kadan. Ana iya cewa yanzu da shi da ita idan ana ta kai ba’a ta kaya.

SABO MUSA: Shi ne shugaban shahararriyar kungiyar nan ta Masari Restoration Awareness Forum kuma babban mai taimaka wa gwamna Masari Kan Dawo Da Martabar Jihar Katsina. Alhaji Sabo ya kwashe sama da shekara arba’in yana gudanar da harkokin siyasa a matakai daban daban. Yana da kyakkyawar alaka da manyan jiga-jigan jam’iyyar APC a jihar Katsina kamar su mai girma gwamna Alhaji Aminu Bello Masari da mataimakinsa Alhaji Mannir Yakubu da kuma jigo a jam’iyyar a jihar Katsina, Alhaji Dahiru Barau Mangal da kuma kungiyoyin matasa. Sabo Musa yana rike da sarautun gargajiya guda biyu Majidadin Magajin Gari da Malumman Bakori. Kalubalen da zai iya fuskanta akwai yanayin dangantakarsa da masu ruwa da tsaki a matakai daban daban. Amma yana da kyakkyawar alaka da jam’ian gwamnati da kuma masu karamin karfi. Ko da yaushe kofar sa a bude take wajen sauraren korafe korafe alumma domin mikawa gwamnati. An shedi shi da taimakon alumma, musamman ga wadanda bas u samun kaiwa ga gwamnati yana zame masu tsani.

SANATA ABBA ALI: Yanzu haka shi ne mataimakin shugaban riko na kasa jam’iyyar APC mai kula da shiyyar Arewa Maso Yamma dake kula da jihohin Kano da Kaduna da Jigawa da Katsina da Sokoto da Kebbi da kuma Zamfara.

Dattijo sanata Abba Ali abokin makarantar shugaban kasa Muhammadu Buhari ne kuma na daya daga cikin na hannun damarsa. Masu sharhi na ganin kamar wannnan damar shugabancin riko na wannan shiyya ta arewa maso yamma wata dam ace ta ya zama zababbaen shugaban jam’iyyar na jihar Katsina.

Alhaji Abba Ali, kwararren dan siyasa ne da aka dade ana damawa da shi, yay i sanata tun lokacin shugaban kasa marigayi Alhaji Shehu Shagari. Duk bait aba furta cewa yana son tsayawa shugabancin jam’iyyar a jihar Katsina ba, amma da dama mutane na has ashen kamar yana son kujerar. Wasu kuma na alakanta shi da takarar gwamna da sanata Hadi Sirika ake kyautata zaton zai iya yi a shekarar 2023 idan Allah ya kaimu.

Kalubalen da zai iya fuskanta akwai yawan shekaru da yake da su, kuma dangatakar da shugabanni da wakilan jam’iyyar APC a matakai daban daban, saboda akwai tazararsa tsakaninsa da al’umma ko masu zabe. Bai rike wani mukamin a kwanakin nan ko dawo war siyasa kuma ba mukamin da ya rike a jihar Katsina.

MALAM KABIR MURJA: Gogaggen dan siyasa ne, wanda shima tsohan dan adawa, bait aba shiga jam’iyyar PDP ba, ana kiransa farfesan siyasa a jihar Katsina. Ya taba tsayawa takarar shugabancin jam’iyyar APC a shekarar 2014, a lokacin yana samun goyan bayan Sanata Injiniya Mahmud Kanti Bello. Haka kuma ya so tsayawa a lokacin da aka tsaida Malam Shitu takarar shugabanci APC, yayin da ya jagoranci tsagen APC Akida, wanda ake kyautata tsammani dan shahararren dan kasuwar nan kuma aminin shugaban kasa, sirikin shugaban kasa Buhari, Abubakar Sama’ila Isah yak e daukar nauyinsa.

Kalubalen da zai fuskanta a wannan karon shi ne wadannan iyayen gida nasa watau Sanata Mahmud Kanti Bello da mahaifin Abubakar Sama’ila duk sun rasu a lokaci mabanbanta. Dole ya sake lissafi, duk da masanin siyasar cin zabe ne, saboda harkar zabe na bukatar masu gida rana ko kuma wanda zai dauki nauyin kashe ma kudin. Wata majiyar ma ta ce jam’iyyar ba ta sabunta katin zamansa dan jam’iyya da ake cikin yi a halin, idan kau har babu katin zama dan jam’iyya babu yadda za’a yi ya tsaya takara shugabancin jam’iyya na kowane mataki , shi yasa ake masu sharhi ke ganin kamar yana da wuyar gaske ya samu nasarar.

Kujerar Shugabancin jam’iyyar APC muna iya cewa za ta iya zama allura cikin ruwa. Saboda na farko dai idan aka ce za’a bi tsarin karba-karba tsakanin shiyyoyin Katsina da Daura da kuma Funtua, nan ma za’a iya zaftare wasu masu Sha’awar tsayawa takarar, akwai yiwuwar kuma ace su masu rike da shugabanci karkashin Malam Shitu da mataimakansa Alhaji Bala Abu Musawa da Mamman Yaro Batsari da kuma Alhaji Usman Osi da zauran shugabanni su ci gaba da tafiyar ragamar jam’iyyar.

Yanzu dai babban abun jira a gani uwar jam’iyyar ta Kasa ta Fito da sharudda da Tsare tsaren yadda za’a gudanar da zaben, wanda har zuwa hada wannan rohatan babu jaddawalin zaben. Kuma akwai yiwuwar nan gaba wasu su kara fitowa ko nuna Sha’awar tsayawa. Saboda su ma wadannan mutane bakwai har yanzu babu wanda ya fito fili ya fara yakin neman a zabe shi kan wannan kujera. Abinda ake jira yanzu a sanya rana da Tsare-tsaren zaben. Lokaci kadai zai tabbatar da wanda ke da rabonta.

Tags: APCHausaKatsinaMasariNews
Previous Post

RASHIN TSARO: An kashe mutum 201, an sace mutum 137 a makon jiya

Next Post

Anya kuwa ‘Yan kudu sun san me ake nufi da kalmar Yaki? Daga Adamu Saleh

Next Post
Anya kuwa ‘Yan kudu sun san me ake nufi da kalmar Yaki? Daga Adamu Saleh

Anya kuwa 'Yan kudu sun san me ake nufi da kalmar Yaki? Daga Adamu Saleh

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • KOWA TA SA TA FISSHE SHI: Ƙoƙarin haɗewar LP da NNPP ya kakare, Peter Obi zai bayyana mataimakin takarar sa ranar Juma’a
  • ‘Da gangar aka bari ƴan bindiga suka kai harin gidan yarin Kuje, saboda na yi ta faɗin hakan zai auku – Mamu
  • Ƴan bindiga sun babbake cibiyoyin kiwon lafiya sun yi dalilin dole aka rufe wasu 69 a Katsina
  • Dala ta ƙara kekketa wa naira rigar mutunci daidai lokacin tsadar kayan abinci
  • Duk da tsananin hare-haren da ya darkaki Najeriya a kwanakin nan Buhari zai waske taro Dakar

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.