• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Su Iyaye Ana Yi Masu Da’a Da Biyayya Ne Har Bayan Ransu, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
May 30, 2021
in Ra'ayi
0
Imam Murtada Gusau

Imam Murtada Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

Assalamu Alaikum

Ya ku bayin Allah! Ku sani, lallai yin biyayya da da’a ga iyaye, a lokacin da suke raye da kuma bayan mutuwarsu, yana daga cikin manyan farillai da wajibai da Allah ya rataya a kan kowane Musulmi, in dai har Musulmin kwarai ne. Kai yana ma daga cikin mafiya girman ayyukan Ibadah, bayan bautar Allah Ta’ala. Allah Subhanahu wa Ta’ala yace:

“Ku bauta wa Allah, kada ku yi masa shirka da komai. Kuma ga iyaye ku kyautata.” [Suratun Nisa’i: 37]

Sannan wata rana an tambayi Manzon Allah (SAW) game da mafiya soyuwar ayukka a wurin Allah, sai ya amsa da cewa:

“Yin Sallah a kan lokacinta. Aka ce sai me? Yace: “Yin biyayya da da’a ga iyaye.” Aka ce sai wane? Yace: “Yin Jihadi a kan tafarkin Allah (wato jihadi na gaskiya, ba irin na ‘yan ta’adda ba).” [Buhari da Muslim]

Kuma Allah Madaukakin Sarki yace:

“Kuma mun yi wasiyyah ga mutum game da iyayensa, mahaifiyarsa ta dauke shi wahala kan wahala ta kuma shayar da shi na shekara biyu, (don haka) ka gode mani kuma ka gode wa iyayenka, (sannan) gare ni makoma take.” [Suratu Lukman: 14]

Da kuma inda Allah yayi umarnin a kyautata masu, musamman idan sun tsufa, yace:

“Ubangijinka Ya hukunta cewa kada ku bauta wa kowa face Shi. Kuma game da iyaye ku kyautata masu, koda dayansu ya tsufa ko dukkansu biyu, kada kace masu tir! Kuma kada kayi masu tsawa (ko ka kwance masu zani a kasuwa), ka gaya masu magana mai dadi. Ka tausasa masu fika-fikan rahama kuma kace: “Ya Ubangiji Kayi masu rahama, Ka tausaya masu, kamar yadda suka rene ni ina karami.” [Isra’i: 23-24]

Kuma Annabi Muhammad (SAW) yayi Allah waddai da wanda bai yi wa iyayensa biyayya da da’ar da zasu kai shi Aljannah ba, yayi addu’a, yace:

“Ya Allah ka turmusa hancinsa, ya Allah ka turmusa hancinsa, ya Allah ka turmusa hancinsa!” Sai Sahabbai suka ce wanene ya Manzon Allah?” Sai yace: “Wanda ya riski mahaifansa lokacin tsufansu, ko daya daga cikinsu ko dukkansu biyu, amma bai shiga Aljannah ba.” [Muslim]

Annabi (SAW) ya nuna cewa rashin da’a da biyayya ga iyaye yana daga cikin manyan zunubai, in da a wani wurin Annabi (SAW) ya nuna cewa, a cikin manyan zunubai, daga shirka sai sabawa iyaye. Wannan yana nuna bayan hakkin Allah sai hakkin iyaye kenan.

Don haka mu sani, kyautata wa iyaye, da da’a da biyayya gare su dole ne, tilas ne, kuma wajibi ne, kuma wannan har bayan ransu, kai ko da ace kafirai ne, wajibi ne ayi masu biyayya a cikin komai da komai, in dai ba sabon Allah da Manzonsa ba ne.

Wajibi ne, kuma wallahi dole ne, duk wani mataki da iyaye suka dauka, ko wani hukunci da suka zartar lokacin rayuwarsu, a tabbatar da shi, ko da bayan ransu ne! Don haka, kar wani da daga cikin ‘ya ‘ya, ya zama dan kuka, ya tayar da wani hukunci, ko wani mataki, da mahaifinsa ya dauka, don kawai yana ganin yanzu baya raye, ko kuma don wani ya tursasa masa yin hakan, ko kuma don kwadayin abun duniya, ko kuma don yana so ya faranta ran wani mutum. Duk kuwa wani da da yayi haka, to ya sani, wallahi, wallahi, wallahi, shi ba dan kwarai bane, ba dan kirki bane, ba dan goyo bane, kuma ba dan arziki ba ne. Domin yin haka yana nuna cewa, YA KWARE WA MAHAIFINSA ZANI NE A KASUWA! Kuma wallahi shima sai Allah ya tayar da wadanda za su yi masa haka, domin a ramawa mahaifin nasa abunda yayi masa na cin mutunci!

Jama’ah wajibi ne a dadada wa iyaye, dole ne a kyautata masu, kuma a kyautatawa duk wanda suke so a kyautata masa, dole ne ayi duk abunda za ya sa suji dadi, su samu natsuwa da farin ciki, a lokacin rayuwarsu da kuma bayan ransu, matukar abin nan ba sabon Allah ba ne da Manzonsa (SAW). Abdullahi (RA) yace:

“Na tambayi Manzon Allah (SAW) cewa wane aiki ne Allah mai girma da daukaka yafi so sai yace: “Sallah akan lokacinta, sai nace sannan wane? Sai yace: Bin Iyaye, sai nace sannan wane? Sai yace: Sannan Jihadi don daukaka kalmar Allah. Sannan yace Annabi (SAW) ne ya fada man wadannan abubuwa muhimmai, kuma da naso ya kara man da ya kara man.”

Abdullahi dan Umar (RA) yace:

“Yardar Allah tana cikin yardar iyaye, kuma fushin Allah yana cikin fushin iyaye.”

Wato wanda iyayensa suka yarda da shi, to Allah za ya yarda da shi, haka ma idan iyayensa suna fushi da shi, to Allah ma yana fushi dashi. A wani hadisin kuma Abdullahi dan Abbas yace:

“Lallai ni ban san wani aiki wanda yafi kusanci zuwa ga Allah ba fiye da biyayya da da’a ga iyaye.” [Duka Hadisan suna cikin Al-Adabul Mufrad, na Imamul Bukhari]

Don haka mu sani, duk mutumin da ya warware wani hukunci, ko wani mataki da mahaifinsa ya dauka, a lokacin da yake raye, wannan mutum ya sani, wallahi yaci amanar mahaifinsa, yaci mutuncinsa, kuma wallahi yayi masa babban butulci, kuma sai Allah ya kama shi akan wannan mummunan aiki da yayi, kuma wannan mutum, da ikon Allah, ba zai taba cin nasara ba a rayuwarsa!

A yau wannan zamani, jama’ah, an wayi gari, wasu daga cikin ‘ya ‘yan wannan zamani, marasa mutunci, suna rungumar makiyan iyayensu a matsayin masoya, ainihin masoyan iyayensu na gaskiya kuwa, sai su dauke su sune makiyansu! Wal iyazu Billah! Wace irin rayuwa ce wannan muke cikin ta don Allah? Yanzu masu yin irin wannan, don Allah suna tsammanin iyayensu zasu samu natsuwa da su, a cikin kabarinsu?

Lallai masu aikata irin wannan ta’asa, su kwana da sanin cewa, yanzu haka, iyayensu suna can cikin kabari, suna tsine masu albarka, kuma suna yin Allah waddai da mummunan aikin da suka yi.

Idan ba dolonci, da wawanci, da miskilanci ba, don Allah ta yaya mutum zai kwancewa ubansa zani a kasuwa, ta hanyar rungumar wadanda suka yi mummunan fada da mummunar adawa da mahaifinsa? Mutanen da duk duniya ta shaida cewa, su ba masoyan ubanka bane; sun zage shi, sun ci zarafinsa, sun bata masa rai, sun nemi su walakanta shi, amma Allah ya kare shi, wai ace wadannan mutane, a yau, sune mutanen ka, da kake mu’amala da su? Wai domin Allah, kai wane irin da ne a wurin wannan mahaifi naka mai daraja?

Mahaifanka da magabatanka sun haife ka, sun yi tarbiyyarka har ka zama mutum, kuma suna zato da tsammanin cewa, zaka kare mutuncinsu da martabarsu, a lokacin rayuwarsu da kuma bayan mutuwarsu, amma ace wai kai ne, za’a hada kai da kai, aci mutuncinsu, a kwance masu zani a kasuwa, a wulakantasu, a mayar da su ba bakin komai ba, saboda ganin basa raye, kuma kayi tsammanin zaka zauna lafiya, zaka gama lafiya, zaka wanye lafiya! Wallahi ba zai taba yiyuwa ba!!

Daga karshe, Manzon Allah (SAW) yace:

“Yana daga cikin cikar biyayya da da’a ga iyaye, mutum ya sadar da zumuncin da ke tsakanin abokai da masoyan mahaifansa.” [Muslim]

Ya Allah, muna rokon ka shiryar da mu tafarki madaidaici, ka nuna muna gaskiya, ka bamu ikon bin ta, ka nuna muna karya, ka bamu ikon guje mata. Ya Allah, ka bamu ikon yin adalci da fadar gaskiya akan ko waye, amin.

Wassalamu alaikum,

Dan uwanku: Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuta daga Okene, jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaIyayeLabaraiNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

KUDU TA DAGULE: An ƙara banka wa ofishin INEC wuta a Jihar Imo, bayan Buhari ya yi tir da kisan Gulak a jihar

Next Post

Ƴan sanda sun kashe makisan Gulak, sun ce mayaƙan IPOB ne suka aikata kisan

Next Post
Ƴan sanda sun kashe makisan Gulak, sun ce mayaƙan IPOB ne suka aikata kisan

Ƴan sanda sun kashe makisan Gulak, sun ce mayaƙan IPOB ne suka aikata kisan

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • HAJJIN BANA: Hankulan maniyyatan Kano 1,238 ya tashi saboda kasa kwashe su kan lokacin rufe filin jirgi Jeddah
  • IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi
  • 2023: Ka zaɓi El-Rufai mataimaki, ‘ka yi nasara a zaɓe kamar yankan wuka’ – Kira ga Tinubu
  • RIKICIN PDP: Kwamitin Amintattun PDP ya tura wa Wike tawagar lallashi
  • KADUNA 2023: Uba Sani ya zaɓi Hadiza Balarabe mataimakiyar sa

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.