Gwamnan Jihar Neja, Abubakar Bello ya bayyana cewa halin da Jihar Neja ke ciki ya yi munin da babu wani bambanci da zamanin yaƙin ‘ƙatilan maƙatulan’, ya ce ya kamata a san cewa yaƙi fa ake yi a Neja.
Bello ya nuna bacin ran sa ne domin ƙara sanar da halin kashe-kashe da hare-haren da ‘yan bindiga ke yi a Neja, tare kuma da sake yin kira ga Gwamnatin Tarayya domin ta kai wa Jihar Neja ɗaukin gaggawa.
Bello ya yi maganar ce ganin yadda hare-hare su ka yi yawa a Ƙananan Hukumomin Rafi, Wushishi da Lavun. Ya ce an kai munanan hare-haren a garuruwan Wushishi, Tegina da Batati.
“Lamarin fa ya yi muni fiye da yadda duk ake tsammani. Maganar gaskiya mun afka zamanin yaƙe-yaƙe. Kuma kamata ya yi a tunkari matsalar nan gadan-adan ba tare da bata lokaci ba.”
Haka Kakakin Gwamnan, Mady Noel-Berje ta bayyana cewa Gwamna Abubakar ya faɗa, cikin wata sanarwa da ta sa wa hannu a madadin gwamnan.
Ya ce za a fara bi gida-gida domin a tabbatar da yawan yara ƙananan da aka sace, aka yi garkuwa da su.
Jami’in gwamnati ya ce ‘yan bindiga kamar su 70 ne su ka karaɗe ƙauyuka 17, a cikin ƙaramar hukumar Wushishi, inda su ka harbi mutane da dama.
An kuma tabbatar da cewa ruwa ya tafi da mata da ƙananan yara, a lokacin da su ka tinjima cikin Kogin Kaduna, domin su tsira daga ‘yan bindiga.
Mutanen da ake nema ba a san inda su ke ba a halin yanzu, ‘yan garuruwan Babako ne da Tashan Jirgi, Kwakwagi,Fakars, Ndiga, Buzu, Akare, Kala Kala, Agwa, Anguwan Gizo, Tsamiya da sauran ƙauyukan da ke maƙautaka da su.” Inji Noel-Berje.
Discussion about this post