A yanzu haka Manyan Hafsoshin Tsaro na Kasar nan na can na ganawa da Manyan Hafsoshin Tsaron kasar nan da kuma sauran shugabannin fannonin tsaro.
Sun amsa kiran gayyatar da Majalisar Dattawa ta yi masu ne, domin su yi bayanin halin da ake ciki kan tabarbarewar tsaro a kasar nan.
Wadanda su ka halarta sun hada da Babban Hafsan Tsaron Kasa, Lucky Irabor, Babban Hafsan Sojojin Kasa Ibrahim Attahiru, na Sama Awwal Gambo da na Ruwa.
Haka kuma cikin sauran manyan shugabannin tsaron akwai Sufeto Janar na ‘Yan Sandan Najeriya, Baba Usman.
Sun shiga dakin taro kuma an kulle kofa wajen karfe 11:06 na rana. Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan ne zai wa manema labarai jawabi bayan sun kammala taron.
Sannan kuma Majalisar Dattawa ta amince shugabannin majalisar su ziyarci Shugaba Muhammadu Buhari domin su tattauna gaskiyar lamarin halin da kasar nan ke ciki, ta yadda za a shawo kan munin da tabarbarewar tsaron ta yi.
Tun a ranar da aka gayyaci shugabannin tsaron, sai da Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan ya yi roko ga sauran santoci cewa idan sun amsa gayyata sun zo yau ranar Alhamis, to idan sun yi kukan rashin isassun kudaden aikin tsaro, to a amince a kasa dumbuza masu.
Najeriya na ci gaba da afkawa cikin mawuyacin halin tabarbarewar tsaro, ta yadda a kullum ana kashe mutane da dama, kuma ana sace wasu masu yawa ana yin garkuwa da su.
Sai dai kuma a ranar Laraba Ministan Yada Labarai Lai Mohammed, ya maida wa jam’iyyar PDP raddin cewa aikin gurfanar da masu garkuwa da mutane da ‘yan bindiga, na jihohin da abin ya yi wa katutu ne, ba aikin gwamnatin tarayya ba ne.
Ya ce gurfanar da ‘yan ta’adda ne aikin gwamnatin tarayya.