• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Hadarin Jirgin Saman Hafsoshin Sojan Najeriya: Ya Zama Wajibi Ayi Kwakkwaran Bincike Na Gaskiya, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
May 22, 2021
in Ra'ayi
0
Hadarin Jirgin Saman Hafsoshin Sojan Najeriya: Ya Zama Wajibi Ayi Kwakkwaran Bincike Na Gaskiya, Daga Imam Murtadha Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

Assalamu Alaikum

Inna lillahi wa inna ilaihi raaji’uun! Jiya juma’ah, 21/05/2021, muka samu wani mummunan labari, marar dadi, mai tayar da hankalin ‘yan Najeriya, na hadarin jirgin saman hafsoshin soja a garin Kaduna, wanda yayi sanadiyyar rasuwar babban hafsan sojojin Najeriya, Janaral Ibrahim Attahiru, da dan uwa, Manjo Janaral Abdurrahman Kuliya, da sauran hafsoshin sojan Najeriya, bayin Allah, masu hazaka, masu bautawa kasarsu tsakaninsu da Allah! Ina rokon Allah Ta’ala ya gafarta masu, amin.

To, su dai wadannan bayin Allah sun mutu, kuma ita mutuwa riga ce ta kowa, kuma wani al’amari ne da yake faruwa ga kowane abu mai rai, dukkan mai rai wallahi za ya mutu. Kuma kowace al’ummah ta yarda cewa kowa sai ya mutu. Musulmi da wanda ba Musulmi ba, kowa yasan cewa lallai sai ya bar duniyar nan, ko yaki ko yaso!

Allah Subhanahu wa Ta’ala ya halicce mu, tare da samar da mu a matsayin masu rayuwa a bayan kasa, domin ya jarraba mu. Allah Madaukakin Sarki yace:

“Shine wanda ya halicci mutuwa da rayuwa domin ya jarraba ku; wane ne daga cikin ku zai fi kyautata aiki.” [Suratul Mulk: 2]

Don haka, duk irin yadda rayuwar mutum tayi tsawo, duk yawan shekarunsa a cikin wannan duniya, duk dadewarsa, duk iya makircinsa, to ko shakka babu, wata rana zai mutu ya koma ga Allah. Kai duniyar nan ma ita kan ta wallahi za ta kare, za ta kuma gushe; dan Adam za’a neme shi ko kasa ko sama a rasa shi, a cikin wannan duniya, zai zama tarihi, ya zamo tamkar ba’a yi shi ba. Abin da kawai zai rage shine, aikin sa, da kuma kirkin da yayi da ayukkansa na alkhairi da ya aikata a lokacin rayuwar sa ta duniya. Rayuwa ta har abada tana gidan lahira. Allah Madaukakin Sarki yana cewa:

“Lallai kuma lahira, tabbas ita ce rayuwa, da sun kasance suna sani.” [Suratul Ankabut: 64]

Annabi Muhammad (SAW), tattare da zamansa mafi soyuwa a wurin Allah, kuma mafi girma da darajar gaba dayan halittar Allah, Allah Ta’ala ya fada masa cewa lallai zai mutu kamar yadda kowane mutum zai mutu.

Sannan shi Manzon Allah (SAW), da gaba dayan halitta, za’a hadu a gaban Allah, a ranar Alkiyamah, domin ayi hisabi a tsakaninsu. Allah Ta’ala yace:

“Lallai ne kai mai mutuwa ne, kuma su ma lallai masu mutuwa ne. Sannan lallai ku, a ranar Alkiyamah, a wurin Ubangijinku, za ku yi ta yin husuma.” [Suratul Zumar: 30-31]

Kuma Allah Madaukakin Sarki ya bamu labarin wasiyar da Annabi Ya’akub (AS) yayi wa ‘ya’yansa cewa:

“Ku sani lallai hakika, Allah ya zabar maku addini, don haka kada ku kuskura ku mutu face kuna Musulmi.” [Suratul Bakara: 132]

Ya ku bayin Allah! Wallahi babu wanda yasan lokacin da ajalin da Allah Madaukakin Sarki ya debo masa zai kare. Babu kuma wanda yasan ko a wane wuri ne Mala’ikan mutuwa zai rutsa da shi. Babu kuma wanda ya isa, ko shi waye, ya canza wannan tsari da shirin da Allah yayi. Allah Madaukakin Sarki yace:

“Kuma ga kowace al’ummah akwai ajali. Sannan idan ajalinsu yazo, ba za’a yi masu jinkiri ba da sa’a guda, ba kuma za su gabace shi ba.” [Suratul A’araf: 34]

Don haka, rayuwar duniya ba komai bace illa wani nau’i na wata gajeruwar tafiya, wadda a karshenta za’a isa gidan lahira.

Ya ku jama’ah! Tun da har Shugaban halitta, Annabi Muhammad (SA) ya dandani zafin mutuwa, to mu sani cewa wallahi kowa ma sai ya dandane ta. Ba wanda zai zauna duniyar nan, ko shi dan gidan waye. Da wanda yayi kisa, ko yasa aka yi kisa, da wanda aka kashe duk mutuwa zasu yi, kuma su hadu a gaban Allah!

Imamul Bukhari ya ruwaito daga Nana Aisha (RA), yadda ta bayar da labarin jinyar da Manzon Allah (SAW) yayi a dakinta, har zuwa rasuwarsa.

Sannan a lokacin da Amru Dan As (RA) yazo rasuwa, an tambayeshi shin yaya yake ji? Sai yace:

“Ji nike yi tamkar sammai sun fado a kai na, kassai kuma sun matse ni.”

Sayyidina Umar Dan Khattab (RA) ya tambayi Ka’abul Ahbar cewa ya siffanta masa yadda mutuwa take. Sai yace:

“Ya kai Sarkin Muminai! Hakika ita mutuwa kamar wani reshe ne mai yawan kayoyi a jikinsa, wanda aka shigar da shi cikin cikin mutum. Bayan kowace kaya ta rike wata jijiya daga jijiyoyin jikinsa, sai kuma a samo wani mutum ma’abucin karfi, ya kama wannan reshen ya fizgo shi da karfi, ya fizgo shi kenan tare da tsoka da jijiyoyin jikin!

Wannan ranar mutuwar fa sai ta riske ni, sai ta riske ka, sai ta riske ki, sai ta riske ku, sai ta riske mu baki dayan mu wallahi, kamar dai yadda ta riski wadanda suka rayu kafin mu.

Wadannan hafsoshin sojojin Najeriya sun rasu, kuma mun yi imani da Allah cewa, lokacin su ne yayi, don haka ba zasu wuce ba. To amma duniya ta shaida, ba zamu boyewa kowa ba, babu munafunci, wallahi muna zargi, kuma zargi mai karfi, cewa kashe su aka yi, domin a binne, ko kuma a boye, ko kuma a dakatar da wasu abubuwa! Don haka, wallahi muna jira, kuma muna sauraro, kuma mun sa ido, ayi bincike, bincike na gaskiya, kuma a sanar da ‘yan kasa sakamakonsa, da kuma sanadiyyar wannan hadarin jirgin saman, domin komai yana da sanadi, da musabbabi!

Gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari, tun farkon hawan ta, tana ware mahaukatan kudade, na fitar hankali, domin sayen makamai a yaki ta’addaci, da magance matsalar tsaro. Kuma ana zargi, kuma zargi mai karfi cewa, an sace kudaden nan, kuma makaman ba’a saye su ba. Domin babu su babu mafarinsu! Irin zargin da ita gwamnatin Buharin tayi wa gwamnatin da ta gabace ta, wato ta Goodluck Ebele Jonathan.

Kuma ana zargin cewa, wannan tuhuma ta sace kudin makamai, a karkashin gwamnatin Buhari, ba’a so aci gaba da shi, shi yasa ake kokarin dakatar da shi ta ko halin kaka, kuma ko da za’a halaka wasu mutane ne!

Sannan da farko, an shedi shi Janaral Ibrahim Attahiru cewa, mutum ne mai gaskiya da rikon amana da tsoron Allah. Shi Mutum ne mai kula da Ibadah sosai, a matsayinsa na Musulmi; kuma a hakikanin gaskiya, an tabbatar da cewa, yana son ya ga bayan ‘yan ta’addan Boko Haram da sauran matsalolin rashin tsaro, da suka addabi kasar nan, domin al’ummar Najeriya su samu zaman lafiya, walwala, da jin dadi. Kuma an yi shaidar shi da cewa mutum ne jarumi, ba ya da tsoro, jarumine na gaske. Dama kamar yadda muka sani, masu son a tabbatar da gaskiya da rikon amana a wannan zamanin, wallahi sun fi kowa shan wahala da fuskantar barazana iri-iri.

Janaral Attahiru yana cikin masu kokarin tona asirin maciya amanar tsaron Najeriya, wadanda suka ci kudin makamai a wannan Gwamnati ta shugaba Muhammadu Buhari, abinda ake ta kokarin ayi rufa-rufa, a bar maganar ta sha ruwa. Shi kuma yaki bayar da hadin kai akan wannan manufa. Hatta ma mai bai wa shugaban kasa shawara akan sha’anin tsaron Najeriya, ya jaddada abinda Janaral Attahiru ya fada, na cinye kudin makamai da aka yi a wannan Gwamnatin.

Hankalin maciya amanar tsaron Najeriya, da ‘yan koren su ya tashi, sai da suka sa shi kansa mai bawa shugaban kasa shawara akan harkar tsaron ya fito ya janye maganar sa, kuma ya janye daga goyon bayan Janaral Attahiru akan batun bacewar kudin makamai.

To yanzu don Allah, kuna tsammanin wadannan mutane, zasu bar Janaral Attahiru, mutumin da suke ganin kamar yana so ya kwance masu zani a kasuwa, ya wanye lafiya?

Jama’ah ku sani! Maciya amanar tsaron Najeriya suna cin riba ne fa da matsalar rashin tsaron nan, don haka basu son matsalar ta kare; saboda haka, ta kowace hanya, suna iya zama sanadiyyar rasa rayuwarsa a hadarin jirgin saman da ya faru da shi jiya, a Kaduna, ya mutu, shi da sauran hafsoshin Najeriya da suka rasa rayukan su tare da shi!

Jama’ah, wallahi ina mai tabbatar maku da cewa, akwai wasu mutane a kasar nan da basu son matsalar Boko Haram ta kare, da sauran matsalolin tsaron kasar nan. Saboda sun mayar da ta’addancin babbar haja ko babbar hanyar neman kudi.

Allah ya sani, ta’addancin Boko Haram da sauran matsalolin tsaron kasar nan, wallahi ko ‘yan sandan kasar nan bai fi karfin su ba, balle uwa uba sojojin Najeriya da aka yi shaidar su da jajircewa da kwazo wurin aiki. Amma sai gashi an wayi gari, kamar matsalar tana nema ta gagari duk jami’an tsaron Najeriya, saboda babu gaskiya cikin lamarin, kuma munafunci yayi yawa!

Ya ku ‘yan Najeriya! Wallahi dole ne a fito ayi magana ta gaskiya, koda za’a mutu. Mun yi imani da Allah cewa duk zamu mutu, bamu zo duniya don mu tabbata ba, don haka bai kamata aci gaba da tafiya haka ba a Najeriya, a kyale maciya amanar tsaron kasar nan suyi yadda suka ga dama!

Wallahi kowa zai mutu, sannan duk wanda yake raye a halin yanzu, babu wanda zai kara shekara dari biyu nan gaba a duniya, face duk muna karkashin kasa. Don haka duk mai shirya makirci don a kashe wani, don Allah kar ya fasa, kuma idan ya isa ya tabbata a cikin wannan duniyar, shi kar ya mutu.

Daga karshe, ina roko, Ya Allah, ka karbi shahadar Janaral Attahiru, da Manjo Janaral Abdurrahman Kuliya, da dukkan bayin Allah da suka rasa rayukan su a wannan hadari. Ya Allah ka gafarta masu, Allah ka yafe kura-kuren su, Allah kayi masu sakamako da Jannatul-Firdausi, Allah ka albarkaci zuri’ar da suka bari, amin.

Sannan ina roko, Ya Allah, ka la’anci dukkanin maciya amanar tsaron Najeriya, Allah ka tona asirin su, Allah ka watsa lamarin su, Allah ka kunyata su, amin.

Dan uwanku, Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuto daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun Imam a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaHausaLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Kotun Tarayya ta jaddada wa jihohi ‘yancin kafa dokar hana karakainar kiwon shanu

Next Post

A bincike musabbabin hatsarin jirgin da ya kashe COAS, Janar Attahiru – Majalisar Tarayya

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
KISAN GILLAR ZABARMARI: Majalisar Tarayya ta aika wa Buhari Sammaci, ya gaggauta bayyana a gabanta

A bincike musabbabin hatsarin jirgin da ya kashe COAS, Janar Attahiru - Majalisar Tarayya

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ‘Yan sanda sun kama mutum 57 da suka kwashe ‘ganimar’ kayan gine-ginen da aka rusa a Kano
  • NUC ta baiwa Farfesa Gwarzo shaidar amincewa da fara karatu a jami’o’in Canadian, Abuja da Franco-British, Kaduna
  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Peter Obi na so kotu ta ba shi iznin yi wa wasu jami’an ICT na INEC tambayoyi
  • TATTALIN ARZIKI: Ɗanyen man Najeriya ya fara kwantai a duniya, bayan Chana, Turai da Indiya sun koma sayen na Rasha mai rahusa sosai
  • HAJJI 2023: Hukumar Alhazai ta gindiya sabbin sharuɗɗan adadin kwanakin ziyara Madina

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.