Wani matafiya ya bayyana cewa bai taba fadawa cikin tsananin tsahin hankali da fargaba ba kamar yadda ya samu kansa ba a hanyar sa ta dawo Kaduna daga Abuja ba.
” Mu fa muna tafiya ne a mota, kwatsam sai muka afka musu a daidai sun gama tattara wasu matafiya, sun lunkuya da su cikin daji.
” Mu ka tsaya cak da yawan mu matafiya har sai da ‘Yan sanda da sojoji suka iso wurin suka dan yi harbe-harben da zasu yi suka bude hanya kafin muka wuce. Amma ciki na da sauran matafiya sun duri ruwa, gaba daya mun fice daga cimin hayyacin mu.
Sanata Shehu Sani shima ya tabbatar da aukuwar wannan al’ amari, inda ya rubuta a shafin sa ta tiwita cewa ” Yanzu wani matafiyi ya kira ni ya ke shaida min cewa masu garkuwa da mutane sun tare hanyar Abuja a daidai Jere zuwa Katari, suna kwashe mutane. Sun tafi da wasu matafiya.
Wani direba da ke sintirin a hanyar koda yashe ya shaida wa wakilin mu cewa, kuda ya iso wannan wuri sai ya iske motoci suna ta juyawa, wasu kuma sun tsaya cak sun zura wa ikon Allah ido.
Daga baya dai jami’an tsaro ne suka zo suka ta bude hanya kowa ya wuce.
Sai dai kuma a wata sanarwa da kwamishinan tsaron jihar Kaduna Samuel Aruwan ya fitar da daren Juma’a ya ce ba a samu rahoton an sace wani a wannan hari na ‘yan bindiga ba,
” Jami’ an tsaro basu tabbatar da sace matafiya a wannan hanya ba, sai dai an ga wasu motoci biyu daya an farfasa su daya kuma babu mutane sai kayan su. Daga baya wadanda ke cikin wancan motan sun dawo, na hondan da aka farfasa gilashin shi ne ba a gan su ba har yanzu”.