A hira da Sa’ada Aliyu ta yi da PREMIUM TIMES HAUSA, ta bayyana dalilan da ya sa ta kirkiro manhajar Helpio, domin kare mata da ake ci wa zarafi musamman a yankin Arewa.
” Shi wannan manhaja ya kunshi inda za ka ga bayana kan menene cin zarafi sannan da yadda za ka iya gane an ci zarafin ta ko shi. Sanna kuma akwai kariya da ke da shi wajen boye bayanan duk wanda ya shiga wannan manhaja domin mika kukan sa.
Sa’ada ta kara da cewa ta kirkiro wannan manhaja ne domin a rika kamo wadanda ke cin zarafin mata a na hukunta su kamar yadda yake a doka.
[youtube https://www.youtube.com/watch?v=c1JVendbSZo&w=560&h=315]
Discussion about this post