Masana’antar Dangote Cement Plc wadda ta fi kowace masana’anta sarrafa simiti a Afrika, za ta kara bunkasa tattalin arzikin Najeriya yayin da za ta damka wa Gwamnatin Tarayya harajin naira biliyan 97 daga cikin cinikin da kamfanin ya yi na siminti daga watan Janairu zuwa Disamba, 2020.
Kiyasi ya nuna Dangote zai bayar da harajin kudin cinikin siminti na naira biliyan 97, adadin rabin kudin da Gwamnatin Tarayya ta raba wa Jihohin kasar nan 35 a cikin watan Janairu, 2021.
Kasuwar simintin Dangote ta karu sosai cikin shekarar 2020 da kashi 12.9 bisa 100, inda sayar da metric tan miliyan 15 cikin 2020.
Sannan kuma kudin shiga sun karu a shekarar 2020, inda aka kamfanin simintin Dangote ya samu kudin shiga har naira biliyan 720.
Duk da cewa an samu cikas a tattalin arzikin duniya sanadiyyar annobar korona, har yau dai Aliko Dangote ya na nan a matsayin sa na bakar fatar da ya fi kowane bakar fata kudi a duniya. Kuma wanda ya fi kowa kudi a Najeriya da Afrika baki daya.
Shugaban Ma’aikatan Dangote Cement PLC, Michel Puchersos, ya bayyana cewa, “shekarar 2020 ta yi wa Dangote Cement kyau sosai, musamman saboda sun fito da sabbin samfuran kayan da su ka samu karbuwa a Najeriya da sauran kasashe. Mun kara yawan wanda mu ke sarrafawa a Najeriya,kuma mun kaddamar da tashar samar da karfin lantarki a masana’antar mu ta siminti da ke Mtwara, Tanzania.
“Wannan kuwa ya sa bayan mun ware kudin harajin da za a bai wa gwamnati, mun samu ribar da ta kai naira biliyan 276.1” Inji shi.