• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Dalilin da ya sa Buhari ya dakatar da Akanta Janar ɗin da ake zargi da kantara satar naira biliyan 80

    Nigerian Pilgrims

    HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai

    Beggars

    Almajirai da mabarata sun kwararo Abuja – Mahukunta

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Dalilin da ya sa Buhari ya dakatar da Akanta Janar ɗin da ake zargi da kantara satar naira biliyan 80

    Nigerian Pilgrims

    HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai

    Beggars

    Almajirai da mabarata sun kwararo Abuja – Mahukunta

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ba ta cire Najeriya daga cikin jerin Kasashen da za su samu allurar rigakafin Covid-19 ba – Bincike DUBAWA

Silas JonathanbySilas Jonathan
February 27, 2021
in Kiwon Lafiya, Rahotanni
0
Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ba ta cire Najeriya daga cikin jerin Kasashen da za su samu allurar rigakafin Covid-19 ba – Bincike DUBAWA

Jam’iyyar PDP a Najeriya ta bayyana a wani rahoto na ta cewa Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) ta cire Najeriya daga cikin jerin Kasashen duniya da za su samu allurar rigakafin Korona, (Covid-19).

Cibiyar gudanar da bincike ta DUBAWA ta bi diddigin wannan magana domin bankado ainihin gaskiya da sahihancin wannan korafi na jam’iayyar PDP a Najeriya.

Zargi: PDP na zargin cewa WHO ta hana Najeriya allurar rigakafin COVID-19

Labarin da jam’iyyar PDP ta bayar cewa Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta hana Najeriya allurar rigakafin COVID-19 bisa rashin cancanta ba gaskiya ba ne. Jami’an WHO sun karyata labarin

Annobar sabuwar cutar COVID-19 ta zo da sabbin matsalolin da hatta kasashen da suka cigaba sai da suka shiga wani hali na ha’ula’i. Daga farkon zuwan cutar, ko kwararru wajen binciken asalin kwayoyin cuta sai da suka dauki lokaci suna bincike kafin suka gano bakin zaren. Sai dai duk da haka, an sami cigaba sosai wajen gano hanyoyin takaita yaduwar cutar da ma samar da rigafin da zai iya kare mutane daga kamuwa da ita.

A ‘yan watannin da suka gabata, wannan cigabar musamman yadda ta shafi kirkiro alluran rigakafin COVID-19 ta janyo cece-kuce da rahotanni mabanbanta dangane da yadda kasashe za su sami allurar. A watan Janairun shekara ta 2021, gwamna Kayode Fayemi shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya ya ce:

“Najeriya na cikin kasashen Afirka goma sha biyun cikin kasashe 92 da aka tantance a matsayin wadanda suka cika sharuddan samun allurar rigakafin. Dan haka za ta sami kason farko a karshen watan Fabrairu.”

To sai dai ba da dadewa ba aka sami bayanan da ke karyata furucin Mr. Fayemi. A shafin Twitter, jam’iyyar adawa ta PDP wadda ta kasance kwakwarar adawa ga jam’iyyar APC mai mulki ta yi zargin cewa hukumar WHO ta cire Najeriya daga jerin kasashen da suka cancanci samun allurar rigakafin. Masu zargin sun ce hukumar ta dauki wannan matakin ne domin gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ta gaza samar da irin wuraren da ake bukata dan ajiye ruwan alluran.

PDP ta wallafa zarginta a shafin twitter tare da wata sanarwa kamar haka:

Fabrairu 6 2021

Sanarwa ga manema labarai

Allurar rigakafin COVID-19: Jam’iyyar PDP ta baiwa Buhari laifi bayan da Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce Najeriya ba ta cancanci samun allurar rigakafin ba.

PDP ta ce hukumar WHO ta cire Najeriya daga jerin kasashen da suka cancanci karbar allurar rigakafin COVID-19, sakamakon gazawar gwamnatin Buhari wajen samar da wuraren ajiye magungunan wanda hakan ya tabbatar da matsayinta na cewa gwamnatin APC ta gaza.

Jam’iyyar ta ce abin kunya ne wanda kuma bai kamata a yafe ba, a ce kasa mai mahimmanci kamar Najeriya ta rasa allurar rigakafin da Hukumar Lafiya ta Duniya ta taimaka a samar. Gazawa da cin hanci da rashawa sun taru sun hana gwamnatin APC samar da wurin ajiyar da ke da sanyin digiri 70 kasa da sifili a bisa ma’aunin selshiyos. Wannan kuma duk da yawan billiyoyin Nerar da ta ce ta kasha wajin yaki da cutar ta COVID-19.

Lallai wannan abun kunya ya sake karfafa matsayarmu na cewa gwamnatin APC ba za ta iya gudanar da gwamnati ba, kuma don haka ne kasarmu ke fama da matsalolin tattalin arziki da zamantakewar al’umma.

A watan da ya gabata jam’iyyar mu ta gargadi gwamnatin Buhari dangane da matakai marasa gamsarwar da ta dauka wajen samun allurar rigakafin da ma sauran abubuwan da suka danganci cutar. Sai dai ta sa kafa ta shure gargadin da duk shawarwarin da muka bayar.

Yanzu ‘yan Najeriya sun shaida da idonsu cewa duk wani ikirarin da ta yi na bayar da kai, ya tsaya a sanarwar da ta yi a kafofin yada labarai. Babu abun da take yi da ya wuce sanar da adadin mutanen da suka kamu da cutar, wadanda suka warke da wadanda suka riga mu gidan gaskiya. Babu matakin da ta dauka wajen binciken cutar, mafarinta da yadda ta ka iya sauyawa ko kuma idan Najeriya na da wani nau’in cutar da ya banbanta da na saura. Sannan ba ta samar da kayayyakin aiki ba, da ma wajen ajiye allurar rigakafin domin kasar ta kaucewa cutar baki daya.

Bugu da kari, wannan ya sake tabbatar da matsayarmu na cewa mambobin kwamitin da shugaban kasa ya baiwa nauyin kula da lamuran da suka shafi cutar wato Presidential Task Force (PTF) ba su cancanta ba. ‘Yan siyasa ne kawai wadanda basu da masaniyar da ake bukata na shawo kan wannan annobar a kasarmu. Ya kuma halatta kiraye-kirayen da ake yi na rusa wannan kwamiti na PTF

Abun takaici ne a ce saboda gazawa da cin hanci da rashawar gwamnatin APC, kasarmu, wadda ta taba kasancewa jagora a matakin kasa da kasa tana kuma gogayya a fannoni daban-daban, yau an wayi gari ta durkushe, hatta abu kankani kamar allurar rigakafi ya gagareta.

Sakamakon wannan lamari mai muni ne muke sabonta kirarmu na rusa kwamitin PTF cikin gaggawa a baiwa ‘yan kasuwa masu zaman kansu damar daukan matakan da suka dace tunda gwamnatin Buhari ta gaza.

Jam’iyyarmu na kira ga duk masu kishin kasarmu da jami’an kiwon lafiya da masu sarrafa magunguna da masu kula da aikin sufuri da su hada kai su taimaka wajen ceto Najeriya daga halin da ta shiga.

Haka nan kuma, PDP tana baiwa shugaba Buhari shawara da ya amince da gazawar gwamnatinsa ya nemi taimako daga kafofin da suka dace sannan ya kwafi matakan da jam’iyyar PDP ta yi amfani da su wajen shawo kan cutar Ebola a matsayin matakin da aka tabbatar zai yi aiki wajen kawar da cutar COVID-19

Sa hannu:

Kola Ologbondiyan, Sakataren Jam’iyya ta kasa

Sanarwar PDP ta dogara da hujja guda daya ne, na cewa WHO ta hana Najeriya allurar domin gwamnati ta gaza samar da wurin ajiya. Dan haka ne wani mai amfani da shafin twitter mai suna Yusuf Yunusa (@yyunusa) ya yi wata tambaya mai cewa:

“Wane ne ke yada wannan labaran karya?”

Dubawa ta binciki kafafe da dama dan tantance ko wannan batu na allurar rigakafin na da gaskiya ko karya ce. Abun da ya sa yin hakan ke da mahimmanci shi ne irin wannan labari zai iya jan hankalin mutane da yawa idan kuma ya kasance karya an yaudari jama’a ke nan. Shi ya sa Dubawa ta dauki nauyin tantance gaskiyar maganar.

Tantancewa

Dubawa ta ji ta bakin Kate Ribet, jami’ar sadarwa a sashin kula da samar da allurar rigakafi na ofishin WHO da ke yankin Afirka sannan ta tambayeta ko Najeriya da gaske ba ta cancanta ba, jami’ar ta ce WHO ba ta hana kowa samun allurar rigakafi a Afirka ba daga COVAX, wadda ita ce hadakar kasa da kasar da za ta tabbatar kasashen duniya sun sami allurar yadda ya kamata.

Bugu ta kari, hukumar WHO na yin iya kokarinta ne ta ga cewa kowa ya sami allurar a kan lokaci.

A yanzu haka ana sa ran duk kasashen Afirkan da suka cancanta, za su fara samun allurar AstraZeneca/Oxford daga karshen watan Fabrairu. Daya daga cikin abubuwan da ke janyo jinkiri shi ne binciken da WHO ke gudanarwa dan ganin ko za a iya amfani da allurar cikin yanayi na gaggawa, kuma nan ba da dadewa ba za’a sami sakamakon wannan binciken.

Daga cikin allurai milliyan 88 da aka baiwa Afirka a matakin farko, kason Najeriya ya fi na kowa yawa domin ta sami milliyan 16.

Ribet ta kuma yi Karin bayani:

“Baya ga kason Astra Zeneca akwai kuma na Pfizer wadanda duk za a iya samu ta COVAX. Da farko Pfizer ta bayar da milliyan daya da dubu dari biyu amma bai kai ko’ina ba. Kasashe 72 suka fara mika bukatarsu ga COVAX kuma kwamitin tantancewa ta amince da 51 (Najeriya ta kasance cikin wadannan kasashe) Daga baya an amince da wasu kasashe 18 su karbi kason Pfizer. A nahiyar Afirka, daga 18 ga watan Janairu, kasashe 13 suka nuna sha’awar samun allurar, daga ciki an amince a fara da guda tara kuma Najeriya ta kasance a cikinsu.”
Dangane da tangardar da aka samu wajen kawo allurar Najeriya ta yi karin haske:

“Mun sami karancin alluran Pfizer saboda haka ba duka kasashe 51 da aka tantance suka samu ba saboda wasu matsaloli. Misali Pfizer ba za ta iya hada kasashe da dama a lokaci daya ba. Dan haka idan aka ce kowacce a cikin kasashe 51 sai sun samu, ba za a cimma abin da ake so ba. Dan haka ta fara mayar da hankali kan kasashen da ke biya daga aljihunsu, sannan aka yanke shawarar daidaita samar da allurar tsakanin masu saye da kudinsu da wadanda ke samu daga yankuna shidda (6) na hukumar WHO.”

Lallai martaninta ya nuna cewa WHO ba ta hana Najeriya samun allurar rigakafin COVID-19 ba. A yanzu haka ma tana jiran zuwan kasonta ne.

Daga Karshe

Sanarwar jam’iyyar PDP cewa WHO ta cire sunan Najeriya daga jerin kasashen da suka cancanci samun allurar rigakafin COVID-19 ba gaskiya ba ne. Jami’ar da ke kula da sadarwa a hukumar WHO ta tabbatar cewa hakan karya ne.

Tags: AbujaDubawaHausaLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

‘Shugaban Kasa na gobe’, haka dubban magoya bayan Okorocha suka rika cewa a Owerri

Next Post

Yaya gaskiyar batun cewa wai ruwan nonon mata na iya kashe kwayar cutar COVID-19? – Binciken Dubawa

Next Post
Yaya gaskiyar batun cewa wai ruwan nonon mata na iya kashe kwayar cutar COVID-19? – Binciken Dubawa

Yaya gaskiyar batun cewa wai ruwan nonon mata na iya kashe kwayar cutar COVID-19? - Binciken Dubawa

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • FASHEWAR TUKUNYAR GAS A KANO: Ministar Jinƙai na so a ɗau matakan hana aukuwar bala’o’i
  • Dalilin da ya sa Buhari ya dakatar da Akanta Janar ɗin da ake zargi da kantara satar naira biliyan 80
  • Hukumar NAPTIP ta cafke matar da ta shahara wajen ciniki da safarar mutane
  • KADUNA TA DAGULE: Boko Haram sun darkako Kaduna, ta’ammali da muggan kwayoyi ya yi tsanani a jihar – El-Rufai
  • 2023: APC ta canja ranakun zaɓen fidda-gwanin ‘yan takara

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.