Gwamnatin Tarayya ta raba naira milyan 80 ga matan karkara 4000 a jihar Neja, wanda aka rana a karkashin Shin Tallafa wa Mata Marasa Galihu a karkashin Ma’aikatar Agaji, Jinkai da Inganta Rayuwar Marasa Galihu.
Gwamnan Jihar Neja, Abubakar Bello, ya bayyana farin cikin sa kan yadda aka raba kudi naira miliyan 80 ga matan jihar su 4,000 a karkashin shirin tallafa wa matan karkara da jari wanda Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa.
Gwamnan ya fadi haka ne lokacin da Ministar Harkokin Jinkai Agaji da Inganta Rayuwa, Sadiya Umar Farouq, ta kai ziyara a jihar a ranar Asabar.
Gwamnan ya ce shirin na ‘Cash Grant for Rural Women’ zai taimaka wa matan jihar da dama wajen ficewa daga kangin fatara da yunwa.
Gwamnan, wanda Sakataren Gwamnatin Jihar, Ahmed Alli, ya wakilta, ya ce tallafin ya zo ne a daidai lokacin da jama’ar Jihar Neja su ke fama da fatara sakamakon hare-haren da ‘yan bindiga ke kai masu ba kakkautawa wanda hakan ya sanya da yawan su sun koma sansanin ‘yan gudun hijira da zama, da satar shanu da kuma annobar korona da ta zo a watannin baya.
Ya ce ya tabbatar matan za su yi amfani da tallafin wajen inganta rayuwar su.
Ya ce, “Na gode wa mai girma Shugaban Ƙasa da ya kawo wannan tsari na taimakon matan karkara a duk fadin kasar nan ta hanyar wannan Tallafi na Musamman.
“Mu na godiya kan dukkan tsare-tsare na Gwamnatin Tarayya da aka ba wannan jiha saboda ambaliya, hare-haren ‘yan bindiga, shirin ‘Conditional Cash Transfer’, ‘GEEP’, ‘N-Power’ da kuma ‘Home Grown School Feeding Programme’ da sauran su.
“Har yanzu mu na bukatar karin taimako a Jihar Neja. Mutanen mu sun kara shiga cikin matsin fatara saboda yanayin rashin tsaro da ‘yan bindiga su ka janyo, da satar shanu da sauran matsalolin rayuwa “Duk da haka, ina tabbatar maku da cewa wadannan matan za su yi matukar amfani da wannan tallafin kudin da aka ba su.”
Tun da farko a wajen kaddamar da shirin a jihar, sai da Minista Sadiya Umar Farouq ta bayyana cewa shirin bada kudin tallafin wani bangare ne na shirye-shiryen gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari na ceto fakirai daga tarkon fatara.
Ta ce, “Ran ka ya dade, a matsayin wani sashe na yunkurin Gwamnatin Tarayya na kawar da fatara da yunwa a fadin kasar nan, an fito da babban Shirin Agajin Jama’a na Kasa, wato ‘National Social Investment Programmes’ (NSIP) da zai inganta rayuwar wadanda su ka fi kowa talauci a kasar nan kuma ya na daga cikin manyan tsare-tsaren yaki da talauci a Afrika.
An tsara shi ne ta yadda za a yi biyan kudi N20,000 sau daya ga matan da su ka fi kowa kasancewa cikin fatara a yankunan karkara a Nijeriya don sama masu hanyar karbar kudin da za su ja jari domin su fara sana’a.
“Ana raba kudin ne ga matan karkara su sama da 150,000 a duk fadin jihohi 36 na kasar nan da kuma Yankin Babban Birnin Tarayya.”
Da ma can ita Jihar Neja an riga an ba ta jimillar kudi N1,991,070,000.00 daga shirin Gwamnatin Tarayya na Tallafin Tiransifar Tsabar Kudi, wato ‘Conditional Cash Transfer’ (CCT), wanda ya shafi rayuwar gidajen mabukata guda 43,611 (PVHHs).
Ƙananan hukumomi 12 da su ka haɗa da Wushishi, Chanchaga, Bida, Kontagora, Rafi, Bargu, Agaie, Mashegu Katcha, Bosso, Munya, Lapai, da Lavun a yanzu duk su na amfana da wannan shirin Gwamnatin Tarayya na CCT a Jihar Neja.
An zao masu cin moriyar shirin bada tallafin kudi ga matan karkara ne daga kananan hukumomi 25 na jihar.
Manyan bai a wajen taron kaddamarwar sun hada da karamin Ministan Harkokin Kasashen Waje Ambasada Zubair Dada, da Darakta Janar na hukumar NEMA, AVM Muhammadu Alhaji Muhammed, da Kakakin Majalisar Dokoki ta Jihar Neja, Abdullahi Wuse wanda shugabar Kwamitin Mata na majalisar, Binta Mamman ta wakilta da sauran su.
Discussion about this post