Kungiyar Kwallon Kafa ta Adamawa United ta makale a Bauchi, ba ta iya komawa Yola ba sannan ta kasa karisawa Kaduna domin wasan ta da Jigawa golden Stars a Kaduna.
PREMIUM TIMES ta gano cewa yan kwallon sun makale ne a Bauchi ne saboda rashin kudin man da zai kawo su Kaduna sannan ka dan karan yunwa da suke ji babu kudin abinci.
” Muna cikin tsananin wahala, duk da cewa gwamnatin jihar na ba kungiyar naira miliyan 12.5 duk wata domin kula da su da kuma tafiye tafiyen mu amma ba su isowa gare mu. Tun da aka raba mana naira N5000 a makonni biyu da suka wuce muci abinci bayan wasn mu da Rivers, ba a sake bamu komai ba sai kwanaki suka bamu nair N2500 mu ci abinci.
” Tsakani da Allah muna wahala ne kawai a Adamawa United, domin muna buga kwallo ne cikin babu abinci. gangandawa kawai muke yi. Ko daga Yola wani ne masoyin kwallo mutumin arziki ya biya mana kudin mota sannan ya biya mana kudin Otel na kwana biyu a Bauchi ” Haka wani dan wasa ya shaida wa PREMIUM TIMES.
Adamawa United ce ke karshe a tebur din kwallon kafa na rukunin kwararru a Najeriya.
Discussion about this post