Ministan Sadarwa Isah Pantami ya bayyana cewa za a iya hada layukan waya dabam-dabam har bakwai da lambar katin zama dan kasa guda daya.
Isah pantami ya fadi haka ne a lokacin ta ya amsa tambayoyi a wani shirin gidan talbijin din Channels dake Abuja.
” Mun kirkiro manhaja da za ka iya hada layuka bakwai da lambarka na katin zama dan kasa nan take cikin sauki. Mun yi haka ne domin a samu saukin hada layukan ba tare da an wahala.
” Sai dai kuma idan aka sake saka dokar ‘Kulle’ a kasar nan, dole kuma jami’an hukuma NIMC da sauran masu ruwa da tsaki a harkar su koma kan teburin a sake sabon lale, ta yadda za a samu nasarar aikin da aka saka a gaba.
” Idan har aka saka dokar ‘garkame mutane’ dole mu bi doka domin muma ‘yan kasa ne. Saboda haka idan gwamnatin tarayya ta sake saka dokar ta baci, ta umarci kowa ya koma gida ya zauna, dole muma mu canja tsari da lissafin mu.
Hukumar NIN ta gargadi kowani dan kasa ya je yayi rajistan kansa domin samin lambar zama dan kasa kuma ya hada layin sa da lambar kafin 9 ga Faburairu.
Discussion about this post