A watan Satumba Kasar Birtaniya ta sanar da bayyanar wata sabuwar samfurin Korona da take mamaye mutanen kasar sannan ana samun karin mutanen kasar da ke ta mutuwa babu kakkautawa da dalilin kamuwa da wannan cuta.
Ita dai wannan nau’in Korona mai suna “lineage B.1.1.7” ta bayyana da tsanani a kasar Birtaniya, yasa dole gwamnatin kasar ta saka sabbin dokoki na dakile yaduwarta da suka hada da dokar shiga da fice da balaguro a fadin kasar.
Sai dai bayan watanni 4 da fadin haka shugaban kwamitin PTF Boss Mustapha ya bayyana cewa an samu bayyanar wannan nau’i na Korona B117 a Najeriya.
Mustapha ya ce masana kimiya sun gano wannan nau’i na cutar ne bayan an dauki lokaci mai tsawo ana gudanar da bincike akan cutar.
“Masana kimiya da kwamitin PTF sun gudanar da bincike akan dalilin da ya sa ake samun karuwa a yaduwar cutar makonnin da suka gabata a kasar nan.
“Sakamakon binciken da masana kimiya suka yi ya nuna cewa akwai burbudin kwayoyin B117 a kasar nan.
A watan Disamba PREMIUM TIMES HAUSA ta buga labarin yadda masana kuma likitoci masu bincike a cibiyar ACEGID, na jami’ar Redeemers dake jihar Osun suka gano wannan nau’i na Korona a gwajin jinin wasu mutum biyu da aka yi wa gwajin Korona.
Shugaban masana kimiyan Farfesa Christian Happi, ya ce ba shi da tabbacin ko wannan nau’i na korona ce yasa ake ta samun karuwar yawan wadanda suke kamuwa da cutar a kasar nan.
Farfesa Happi ya ce ba zai iya tattabar da ko sabuwar Koronar bace take yaduwa kamar wutar daji a kasar nan saboda an gano ta tun a watan Oktoba ne, wanda a lokacin ba a samu yaduwar ba kamar yadda ake samu a watan Disamba.
Shugaban hukumar NCDC Chikwe Iheakweazu ya bayyana cewa a yanzu dai ana jiran shawarar hukumar kiwon lafiya ta Duniya, WHO game da wannan nau’i na Korona.
Gwamnati ta yi kira ga mutane a ci gaba da bin dokokin samar da kariya daga kamuwa da cutar ta hanyar saka takunkumin fuska, yin nesa-nesa da juna da kuma kula da lafiyar jiki.
Discussion about this post