• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Nadin Sabbin Manyan Hafsoshin Tsaro Haramtacce Ne, Ya Kauce Wa Doka -Lauyoyi

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
January 29, 2021
in Manyan Labarai
0
Nadin Sabbin Manyan Hafsoshin Tsaro Haramtacce Ne, Ya Kauce Wa Doka -Lauyoyi

Lauyoyi daban-daban sun bayyana cewa nadin da Shugaba Muhammadu Buhari ya yi wa sabbin Shugabannin Tsaro na sojojin Najeriya haramtacce ne, domin ya karya Dokokin Najeriya kuma ya yi fatali da abin da Kundin Dokokin Sojojin Najeriya.

A ranar Talata ce dai aka nada sabbin shugabannin tsaron Najeriya kuma su ka gana da Shugaba Muhammadu Buhari a ranar Alhamis, su ka kama aiki a ranar Alhamis din.

Shugaba Muhammadu Buhari ya gargadi sabbin Shugabannin Tsaron Kasa da su kasance masu kishin kasar su tare da yi wa kasar su aiki bakin-rai-bakin-fama.

Ya yi wannan kira da kuma gargadi a gare su a ganawar farko da ya yi a su a Fadar Shugaban Kasa, a ranar Laraba, wadda ita ce ganawar farko tun bayan nada su da ya yi a ranar Talata.

Ministan Tsaro Bashir Magashi ne ya jagorance su a wajen taron, wanda shi ma tsohon soja ne da ya yi ritaya ya na Manjo Janar.

Cikin wata sanarwa da Kakakin Yada Labarai na Shugaba Buhari ya fitar bayan ganawar ta su, Femi Adesina ya ce Buhari ya gargade su cewa sai fa sun tashi tsare, domin Najeriya na cikin halin ta-baci, wato an shiga ‘la haula wa la kuwwata’ a matsalar tsaro.

“Mu na cikin halin ‘la haula wa la kuwwata. Sai kun jajirce sosai kun yi wa kasar nan aiki tukuru. Saboda ku fa dama biyayyar ku ba wani ku ke wa ba, sai kasar nan kawai.”

“Babu wani abu da zan iya fada maku dangane da aikin soja wanda ba ku sani ba. Domin har yanzu a cikin sa ku ke. Sannan ina tabbatar maku duk wani abu da zan iya yi a matsayi na na Babban Kwamandan Askarawan Najeriya, to zan yi maku domin ku kai ga nasarar da jama’a za su yi murna da ku.

“Kun san dai halin da mu ka tsinci kan mu a 2015 lokacin da mu ka karbi mulki. Kun kuma san halin da mu ke a yanzu. Kuma ku na sane da alkawarin da mu ka yi wa jama’a. Mun yi masu alkawarin samar da tsaro a kasar nan. Duk abin bai zo mana da sauki ba. Amma dai mun samu ci gaba bakin gwargwado.”

Lauyoyin da su ka yarda su ka yi magana da PREMIUM TIMES sun bayyana cewa kwata-kwata nadin sabbin shugabannin tsaron ya kauce wa Dokar Najeriya da gaba dayan kundin dokar na 1999. Har ma da Dokar Sojji ta Najeriya.

Babban Lauya dan rajin kare hakkin jama’a, Femi Falana ya bayyana cewa ya na mamakin irin wannan gurunduma da Shugaba Muhammadu Buhari ya yi, inda ya nada sabbin shugabannin tsaro, ba tare da amincewar Majalliasar Tarayya ba.

“Don haka wannan a maganar gaskiya kamar yadda doka ta tanadar, ba nadi ba ne, bayyana sunayen su kawai ya yi. Ba za su zama halastattun shugabannin tsaro ba, har sai ranar da Majalisar Tarayya ta amince da su tukunna.”

Falana ya ce kamata ya yi a ce an bi doka, a Buhari ya mika sunayen su ga Majalisar Dattawa, su kuma su gayyace su omin su tantance su daya bayan daya.

Falana (SAN) ya ce a ka’idance kuma a dokance, har yanzu nadin su bai tabbata ba tukunna, har sai Buhari ya mika sunayen su ga Majalisar Dattawa an tantance su tukunna. Kamar dai yadda kundin tsarin mulkin Najariya da kuma Kundin Dokokin Aikin Sojan Najeriya su ka shimfida.

“Wannan abu karara haka ya ke, Buhari ya tabka barababiya da shirme. Ba su tabbata ba har sai Majalisar Dattawa ta Tantance su tukunna. Kuma Buharin ne da kan sa zai aika da sunayen su ga Majalisa, sannan a gayyace su domin a tantance su.

“Irin haka ta faru inda cikin Festus Keyamo, wanda a yanzu Minista ne a karkashin mulkin Buhari, ya kai kasar Shugaban Kasa cikin 2008, a shari’a mai lamba FHC/ABJ/CS/611/2008.”

“A hukuncin da Mai Shari’a Adamu Bello ya ce haramun ne Shugaban Kasa ya nada Shugabannin Tsaron Kasa haka kawai kai-tsaye, ba tare da ya fara tura sunayen su Majalisa ta tantance ba. Saboda haka doka ta Sashe na 18 (1) & (3) na Dokar Sojan Najeriya ta shimfida.”

Sannan kuma Falana ya ce wancan hukunci da aka yanke ya zauna, ya kara tabbata doka, domin Gwamnatin Tarayya ba ta daukaka kara ba.

Shi ma wani lauya Jiti Ogunye, tun a cikin wani ra’ayi da PREMIUM TIMES ta buga cikin 2014, ya bayyana cewa Shugaban Kasa radin kan sa shi kadai ba shi da iznin nada shugabannin tsaro, har sai ya fara aikawa da sunayen su Majalisar Dattawa ta tantance tukunna.

Ya yi rubutun ne ganin yadda a cikin 2014 tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya nada Alex Bade Babban Hafsan Tsaron Kasa.

Sai dai ba a sani ba ko Shugaba Buhari ya aika da sunayen a Majalisa. Idan ma ya aika, to ba a dai tantance su din ba.

Kakakin Yada Labarai na Shugaban Majalisar Dattawa, Ola Awoniyi, ya shaida wa PREMIUM TIMES cewa ba shi da masaniyar ko an aika da sunayen.

An tuntubi Keyamo dangane da karar da ya taba kaiwa kan nada Hafsoshin Tsaron Kasa ba bisa ka’ida kuma ya yi nasara.

Keyamo wanda a yanzu Minista ne a Gwanatin Buhari, ya ce ya na nan kan goyon bayan wancan hukunci da kotu ta yanke a lokacin.

A lokacin dai, baya ga haramta nadin da aka yi, kotun ta kuma haramta wa kowane shugaban kasa na Najeriya sake nada shugabannin tsaro ba tare da fara mika sunayen su majalisa ta tantance ba tukunna.

Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa neman amincewa da sabbin Shugabannin Tsaro

Shugaba Muhammadu Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa wasikar neman amincewar su da sunayen manyan hafsoshin sojoji hudu da ya nada matsayin Shugabannin Tsaron Kasa.

Ya nada su a ranar Talata, jim kadan bayan sauke su Janar Buratai a ranar.

PREMIUM TIMES ta buga labarin cewa Buhari ya tsige Buratai da sauran Manyan Hafsoshin Tsaro, ya nada sabbi

Shugaba Muhammadu Buhari ya amince da takardar sanarwar ajiye aiki da Manyan Hafsoshin Tsaron Kasa su hudu su ka yi.

Wadanda su ka ajiye aikin sun hada da Hafsan Hafsoshin Sojoji, Tukur Buratai, Babban Hafsan Tsaron Kasa, Janar Abayomi Olonisakin, Babban Hafsan Sojojin Ruwa, Vice Admiral Ibok Ibas da kuma Air Marshal Sadique Abubakar, Babban Hafsan Sojojin Sama.

Wata sanarwa da Kakakin Yada Labarai na Shugaba Buhari, Femi Adesina ya wallafa a shafin sa na Facebook, ta ce Buhari ya yi wa hafsoshin fatan alheri a dukkan al’amurran da su ka sa gaba bayan ritayar da su ka yi.

An maye guradun su da Manjo Janar Leo Irabor, matsayin Babban Hafsan Tsaron Kasa, Manjo Janar I Attahiru, matsayin Babban Hafsan Sojoji wanda ya canji Buratai, Rear Admiral A.Z Gambo, Babban Hafsan sojojin Ruwa, sai kuma Air-Vice Marchal I.O Amao, Babban Hafsan Sojojin Sama.

Buhari ya taya sabbin manyan hafsoshin kasar da ya nada murna, kuma ya yi horo gare su su kasance masu biyayya da aiki tukuru kan ayyukan da aka dora wa kowanen su.

Cikin wata sanarwa da Mashawarcin Musamman A Fannin Majalisar Dattawa, Babajide Omoworare, ya ce Buhari ya aika da wasikar ga Shugaban Majalisar Dattawa tun a ranar 27 Ga Janairu.

Ya ce an yi haka kamar yadda Sashe na 18 (1) na Dokar Aikin Soja ta Najeriya ta tanadar.

Ya ce ba gaskiya ba ne da ake cewa an nada su ba tare da an sanar da Majalisar Dattawa ba.

Tags: AbujaBuhariFemi AdesinaKakakinLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa neman amincewa da sabbin Shugabannin Tsaro

Next Post

Buhari ya gargadi masu hankoron ruruta gabar addinanci da kabilanci

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Dole manoma su zage damtse bana, gwamnati bata da kudin shigo da abinci daga waje – Buhari

Buhari ya gargadi masu hankoron ruruta gabar addinanci da kabilanci

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ƘARFIN HALI: Na san Kwankwaso na Villa yau, amma da mun haɗu da na gaura masa mari – Ganduje
  • ‘Yan sanda sun kama mutum 57 da suka kwashe ‘ganimar’ kayan gine-ginen da aka rusa a Kano
  • NUC ta baiwa Farfesa Gwarzo shaidar amincewa da fara karatu a jami’o’in Canadian, Abuja da Franco-British, Kaduna
  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Peter Obi na so kotu ta ba shi iznin yi wa wasu jami’an ICT na INEC tambayoyi
  • TATTALIN ARZIKI: Ɗanyen man Najeriya ya fara kwantai a duniya, bayan Chana, Turai da Indiya sun koma sayen na Rasha mai rahusa sosai

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.