• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

KUSHEWAR BADI SAI BADI: Siradi 10 Da ’Yan Najeriya Su Ka Tsallake Kafin Shiga 2021

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
January 1, 2021
in Babban Labari, Rahotanni
0
Mutum 9 cikin 10 a jihohin Sokoto, Taraba da Jigawa fakirai ne tuburan – Rahoton NBS

Bayyanar cutar Korona a karon farko a Najeriya a ranar 27 Ga Fabrairu, ya gigita kasar nan. Ga duk dan Najeriya ya fahimci cewa akwai wani babban lamari kuma mummuna da ke neman mamaye duniya, ba ma Najeriya kadai ba.

Watan Maris na shigowa al’amurra su ka murde wa Najeriya, su ka dagule, su ka daburce su ka damalmale. Ya zuwa ranar 27 Ga Maris, 2020, tuni ’yan Najeriya sun fara gudun kowa ta sa ta fisshe shi, saboda sanarwar za a kulle wasu jihohi, musamman Lagos da Abuja, sakamakon fantsamar da cutar korona ke kara yi.

Mako daya bayan wannan, sai kasa ta dagule, arankatakaf din ta. Daga labarin kulle tashoshin jiragen sama, sai labarin kulle tashoshin ruwa. Sai batun kulle Lagos da Abuja. Sai hana zirga-zirgar motoci. Sai dokar kulle mutane su na zaman gida tilas. Sai kulle masallatai da coci-coci, kasuwanni da wuraren cin abinci da na shakatawa.

Tun daga nan milyoyin jama’a su ka shiga kuncin rayuwar da har yau idan wasu sun fita, to wasu ba su fita daga kuncin ba.

Yayin da ’yan Najeriya masu tsawon rai su ka kai ga shiga shekarar 2021, ko tantama babu za a iya kiran waccan da aka tsallake, wato 2020, shekarar da kyar na sha ya fi da kayar aka damke ni. Dalili, ai ba cutar korona kadai ce manyan kalubalen da su ka dabaibaye kasar ba.

Abin ne da yawa, wai ‘mutuwa ta je kasuwa’. Amma dai ga wasu muhimman siradan da ’yan Najeriya su ka tsallake kafin su shiga shekarar 2021.

Cutar Korona: Allah kadai ya san yawan mutanen da korona ta kashe a duniya, baya ga wadanda alkaluman kididdiga su ka bayyana. A Najeriya mutane da yawa na su zuwa gwaji. Wani ya kamu da cutar ya warke, wani kuma ta kama shi ya bingire. Mace-mace da dama ba a fito an bayyana musabbabin su ba.

Sai dai kawai inda mutum zai kara firgita, idan ya ga fitattu ko mashahuran ‘yan Najeriya da cutar ta kashe a cikin 2020.

Korona ta kashe majiyyaci ta kashe mai jiyyar sa. Ta kashe dimbin jami’an kula da llafiya, kuma ta kama dubbai a kasar nan.

Mutanen da su ka mutu ba ta musabbabin cutar korona ba, su na da dimbin yawa. Duk wanda ya ga jerin wasu mashahurai ‘yan asalin Jihar Jigawa da su ka bar duniya cikin 2020, tabbas abin zai tabbatar masa da cewa duk wanda ya tsallake 2020, ya cancanci a kira shi mai rabon ganin badi. Ko a Jajibirin sabuwar shekara, wato ranar 31 Ga Disamba, 2020 an yi rashin mahaifin tsohon Ministan Harkokin Waje, dan asalin Jihar Jihar Jigawa, Nuraddeen Mohammed.

Boko Haram: Cikin shekarar 2020 dai Boko Haram ba su jefa bama-bamai sosai ba. Amma fa sun yi mummunan kisa. Su tare hanya su kashe. Su yi wa garuruwa tattaki su kashe na kashewa. Su kai wa sojoji hari su kashe na kashewa. Ba sau daya ba sun kashe sama da mutum 30 ko 40 a lokaci guda.

Bala’in ta’addancin Boko Haram na ci gaba da karuwa a jihar Barno, la’akari da cewa ta’addancin ya koma reshe biyu, wato bangaren tantagaryar ‘yan Boko Haram, su Shekau da kuma rundunar ‘yan ta’addar ISWAP masu rassa a wasu kasashe, amma duk buri daya su ke neman cimmawa su da su Shekau din.

Su kan su Hukumomin Tsaro na Sojojin Najeriya sun bayyana cewa cikin watanni 10 na 2020, wato tsakanin Maris zuwa Disamba, Hukumar Tsaro ta Sojojin Najeriya ta tabbatar da cewa a cikin shekarar 2020, tsakanin ranar 18 Ga Maris zuwa 30 Ga Disamba, sojoji sun ‘markade’ tantagaryar mabarnata 2,403 a fadin kasar nan.

“Baya ga wadannan masu laifi 2,403 da aka ‘makade’, Enenche ya kara da cewa a yankin Arewa maso Yamma an kwato dabbobi 5,281 da kuma albarusai 6,951 sai kuma bindigogi 120 masu samfuri daban-daban daga hannun ’yan bindiga.

“Banda wadannan kuma akwai wasu ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga da dama wadanda aka ‘narkar’ da su a hare-hare ta amfani da jirayen yaki.” Inji Enenche.

Ya kuma yi bayanin cewa a cikin wadannan watanni 10, sojoji sun ceto mutane 864 da aka yi garkuwa da su a jihohi daban-daban a fadin kasar nan.

Daga wadannan bayanai, mai karatu zai tabbatar da cewa ba a ma san iyakar rayukan da aka kashe cikin Najeriya a shekarar 2020 ba.

Garkuwa Da Mutane: Da Kyar Na Tsere Ya Fi Da Kyar Aka Damke Ni

Bala’in da Najeriya ta tsinci kan ta dalillin buwayar masu garkuwa da mutane, ya ma sa ba’arin milyoyin al’ummar kasar nan sun daina jin tsoron cutar korona. Abin da ya fi damun su a yanzu shi ne yadda masu garkuwa su ka fi karfin hukuma.

A kullum idan Boko Haram ba su kama matafiya sun yi garkuwa da su ba, to ‘yan bindiga za su tare hanya su kwashi matafiya su nausa cikin daji da su.

Har yau ba a kididdige yawan jama’ar da aka yi garkuwa da su a jihohin Kaduna, Katsina, Zamfara, Sokoto, Neja da sauran jihohi ba. Ba a kuma san adadi ko naira bilyan nawa masu garkuwa su ka karba a matsayin kudin fansa a cikin 2020 ba.

Sun buwayi kauyuka sun buwayi garuruwa. Sun buwayi dazuka sun buwayi manyan titina. Ta kai a yau ka tambayi dan Arewa ya shaida maka abin da ya fi tsoro, tashin farko zai ce maka masu garkuwa da mutane.

Babab mutum komai mukamin sa, ce maka zai yi ya fi jin tsoron bin hanyar Kaduna zuwa Abuja. Gwamna na tsoron bin hanyar haka sarki. Jami’an tsaro na tsoron bi, haka su ma malamai. Talaka na tsoro haka attajiri.

Cikin karshen shekarar nan ne fa aka yi garkuwa da dabilai jimlar 423 a Jihar Katsina. Yayin da Boko Haram su ka kassara Arewa maso Gabas, su kuma masu garkuwa sun kassara yankunan Arewa maso Yamma musamman Katsina, Sokoto, Zamfara, Kaduna da Neja.

Allah kadai ya san yawan wadanda aka yi garkuwa da su a cikin 2020. Kuma da yawa sun mutu a hannun masu garkuwa, an bindige su bayan an kai kudin fansa, ko kuma bayan an kasa kai kudin fansa.

Shi kuwa wanda ya kubuta daga hannun masu garkuwa da kuma wadanda ke addu’a kada Allah ya sa su da masu garkuwa su ga juna, za a iya cewa sun tsallaka cikin 2021 a halin da Bahaushe ke cewa, ‘da kyar na tsere, ya fi da kyar aka kama ni.’

Tsadar Rayuwa: Shekarar 2020 ta haifar wa ’yan Najeriya da tsananin kuncin rayuwa. Wasu dalilan sun hada da Hare-haren Boko Haram masu kashe mutane, su kwashe dukiyoyin su, sai masu garkuwa da ke karbe ilahirin dukiyar mutum da ta dangin sa kafin su sake shi. Da yawa ma gidajen su ake sayarwa a biya masu garkuwa kudin. Ga kuma dabbobi da kayan abinci da masu garkuwa ke kwashewa jama’a.

Da yawan mutanen kauye sun samu damar tsallake siradin 2020 su ka tsallako 2021 a yau, saboda sun yi hijira daga kauyukan su sun koma birane da zama. Saboda tsoron ’yan bindigar da su ka gagari gwamnati.

Akwai kuma dalili na game-gari, wato kullen zaman gida tilas da aka yi na tsawon watanni sakamaon fantsamar cutar korona.

Karyewar tattalin arziki a lokacin korona, ta yadda har sai da ta kai farashin gangar danyen man fetur a kasuwannin duniya ya koma daidai da farashin ruwan askin cikin kofin wanzami. Wannan ma ya haifar da matsalar karayar tattalin arziki.

Zaman dirshan da aka rika yi a gida ya haifar da fitintinu, musamman bas ace-sace da yi wa cin zarafin mata.

Tsadar Kayan Abinci:

Hana shigo da kayan abinci daga kan iyakokin Najeriya da kullle kan iyakokin sukutum ya haifar da matsanancin tsadar abinci. A cikin 2020 sai da ta kai shinkafar da ake nomawa a cikin kasa ta gagari talaka. Duk abin da ka taba za ka ji ya yi tsada. Kwanon shinkafar da aka sayarwa naira 500 kafin hawa mulkin Buhari, yanzu haka har ranar jajibirin shiga 2021 naira 1500 ake sayar da shi.

Saura nau’ukan kayan kayan abinci irin su gero, garin kwaki, masara, wake, dawa sun yi tsada matuka. Aka wayi gari akusan karshen 2020, sai da albasa ta nemi gagarar hatta masu karfin su kan su. Buhun da a da ake sayarwa naira 17,000, sai da ya dangana da naira 47,000, wasu jihohin ma har naira 50,000.

Gidajen da aka shekara 20 ba a ci shinkafar Hausa ba, sai ga shi sun shafe shekarar 2020 ba su ci shinkafar Thailand mai kyau ko da a rana day aba. Farashin buhun shinkafa ya zama kudin jarin fara wata sana’a mai kwari.

Yayin da gwamnatin Buhari ke bai wa masu karamin karfi tallafi na lamunin jarin naira 20,000 domin kama sana’a, kwata-kwata kudin bai kai kudin buhun shinkafa ba.

Shi kan sa Shugaba Buhari ya san ana cikin halin matsi da kuncin rayuwa sanadiyyar tsadar kayan abinci. Domin ko a cikin makon karshe na shekarar 2020, ya sha aradun cewa zai magance tsadar kayan abinci cikin 2021 a kasar nan.

Tsadar Man Fetur: Kuncin rayuwa da aka shiga cikin 2020 bai hana gwamnati rika kara wa litar man fetur kudi ba. har sai da ya dangana da naira 167. Ba fetur kadai aka kara wa kudi ba. Ita ma wutar lantarki an kara mata kudi. Wannan lamari ya bai wa kowa mamaki da kuma al’ajabi, ganin yadda Gwamnatin Buhari ta rika karin kudin fetur a lokacin da ake cikin halin kuncin tsadar rayuwa.

2020: Shekarar Takunkumi: Wannan shekara dai ta karya alkadarin wata karin magana da Bahaushe ke cewa, ‘takunkumi sai kura!’ Annobar korona ta sa a duniya kaf an koma daura takunkumi a baki da hanci. Tun kafin watan Maris ya yi nisa tuni takunkumi ya mamaye biranen kasar nan. Kowa ka gani daure da takunkumi, tamkar kura a hannun gardi. A yau ta kai ta kawo tun Shugaba Buhari ba ya daura takunkumi, har ta kai yanzu ta kai shi ga daurawa tilas.

A karshen 2020 ma abin ya yi zafi sosai, har gwamnatin Jihar Kaduna da Gundumar Babban Birnin Tarayya Abuja, sun fara cin tarar naira 20,000 ga duk wanda ya fito bai daura takunkumi a bakin sa ba.

Shekarar 2020 ta hana abubuwa da yawa. Ta hana zumunci, ta hana musabaha hannu da hannu. Har yau Buhari ba ya gaisawa da kowa, sai dai su hada damtsan hannaye, kamar ‘yan dambe. Wannan ita ce sabuwar nau’in gaisawar da aka tsallako cikin 2021 da ita.

2020: Shekarar Cinikin Mutum Kamar Cinikin Akuya A Kasuwa:

A wannan shekara ce masu garkuwa da mutane su ka fi cin kasuwar cinikayyar mutanen da su ke kamawa. Yadda ake cinikin wata babbar kadara, haka ake ciniki tsakanin dangin wanda aka kama da masu garkuwa. Idan ba su sallama ba, a bar cinikin sai gobe idan an kara taya wa. Ba a taba ganin irin wannan bala’i kamar cikin 2020.

Shi ya sa ake ganin masu garkuwa da mutane sun fi karfin gwamnati, domin har zaman sulhu da neman sassauci gwamnatin ke yi da su.

2020: Shekarar Karin Karin Haraji: Cikin wannan shekara haraji nau’I daban-daban ya karu. Kuma an kirkiro wasu. Duk wannan ya faru ne saboda rashin kudade a hannun gwamnati. Harajin-jiki-magayi (VAT) ya karu. An kirkiro harajin ladar-ganin-ido, wanda ko kadara mutum zai sayar, sai ya fitar wa gwamnatin tarayya haraji a cikin kudin. Ga kuma harajin-la’ada-waje, wanda ko haya mai gidan haya ya bayar da gidan sa, sai ya cire wa gwamnatin tarayya haraji a cikin kudaden.

Kasancewa Kasafin 2021 na naira tiriliyan 13.588 ya zama riwayoyin da bas u da tabbas, domin babu kudin babu alamar su, a ranar karshe ta 2020 Buhari ya gargadi Shugabannin Hukumomin Tara Kudaden Haraji cewa duk wanda bai tara kudi daya a 2021 ba, to zai tara masa gajiya.

Shekarar 2020 ta zama shekarar da a tarihin kasar nan aka fi ciwo bashi daga kasashen waje.

Kuma wannan shekara ta 2020 ta zo da ibtila’in Tarzomar #ENDSARS, wadda tun bayan yakin Basasa ba a taba yin tarzomar da ta haifar da asarar dukiya kamar ta ba.

Ita kan ta kasar ta shiga tangal-tangal a cikin 2020, domin kadan ya rage da tarzomar #ENDSRARS ya tarwatsa ta. Watakila da a cikin 2021, sai dai a bayar da wani labarin daban, ba irin wannan ba.

Yayin da ’yan Najeriya su ka shiga 2021, babu mai fatan sake maimaita abubuwan da su ka faru cikin 2020.

Tags: AbujakoronaLabaraiNajeriyaPREMIUM TIMES
Previous Post

KORONA: Legas, Abuja da Kaduna suka fi yawan wadanda suka kamu ranar Jajibarin 2021 cikin mutum 1,031 da suka kamu

Next Post

2021: Shekarar kawo karshen da matsalolin da suka zame mana kashin kifi a wuya – Buhari

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
2021: Shekarar kawo karshen da matsalolin da suka zame mana kashin kifi a wuya – Buhari

2021: Shekarar kawo karshen da matsalolin da suka zame mana kashin kifi a wuya - Buhari

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Ƴan sanda sun ceto yara 9 da aka yi garkuwa da su a Zamfara
  • FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air
  • Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto
  • CIRE TALLAFIN MAI: ‘Yan Najeriya na dandana tsadar kayan abinci da motocin sufuri
  • TASHIN HANKALI: Saboda lalacewa yanzu, har Nas-Nas na fede mutum asibitoci

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.