Hukumar NCDC ta sanar da karin mutum 1,617 da suka kamu da cutar Korona a Najeriya ranar Litini.
Alkaluman da hukumar NCDC ta fitar ranar Litini sun nuna cewa Legas ta samu karin mutum –776, Kaduna-147, Kwara-131, FCT-102, Filato-78, Edo-59, Ogun-53, Osun-45, Rivers-37, Taraba-36, Nasarawa-34, Adamawa-33, Kano-26, Delta-20, Ebonyi-16, Bayelsa-11, Gombe-11 da Borno-2
Yanzu mutum 112,004 suka kamu da cutar a Najeriya, mutum 89,939 sun warke, 1,449 sun rasu. Sannan zuwa yanzu mutum 20,616 ke dauke da cutar a Najeriya.
A ranar Lahadi, mutum 1444 suka kamu a Najeriya, jihohin Legas, Filato, Kaduna, Ebonyi, Akwa Ibom da Babban birnin Tarayya, Abuja ne suka fi yawan wadanda suka kamu.
Har yanzu dai jihar Legas ne ke da mafi yawan wadanda suka kamu da mutum –41,400, FCT–14,700, Filato –6,831, Kaduna–6,325, Oyo–4,695, Rivers–4,429, Edo–3,320, Ogun–2,912, Kano–2,617, Delta–2,122, Ondo–2,070, Katsina–1,723, Enugu–1,583, Kwara–1,697, Gombe–1,500, Nasarawa–1,335, Ebonyi–1,275, Osun–1,260, Abia–1,134, Bauchi–1,107, Borno–867, Imo–857, Sokoto – 677, Benue 657, Akwa Ibom–667, Bayelsa 608, Niger–547, Adamawa–573, Anambra–515, Ekiti–473, Jigawa 425, Taraba 294, Kebbi 251, Yobe-211, Cross River–169, Zamfara 162, Kogi–5.
Cibiyar Binciken Lakanin Hada Magunguna ta Kasa, NIPRD, ta bayyana cewa ta gano wasu sinadarai da lakanin da idan an harhada za a iya samar da maganin warkar da cutar Korona.
Sai dai kuma Babban Daraktan Cibiyar Pharmaceutical Research and Development (NIPRD), Obi Adigwe ne ya bayyana haka yayin da ya kira wani taron manema labarai a ranar Litinin, wanda PREMIUM TIMES ta da cikakken bayanin da daraktan ya gabarar.
Adigwe ya bayyana cewa sun gano lakani sadidan wanda wato ‘Nipprimmune’, wanda gidigat ne kuma sadidan zai yi maganin cutar korona.
Sai dai kuma ya yi korafin cewa rashin tallafin kudaden aikin bincike da hada maganin zuwa ruwan allura ko kwayoyi ne cikas din da su ka hadu da shi.
“Tun kimanin tsawon shekara daya kenan, mu ka yi amfani da kwarewa da kuma fasahar kimiyyar da muka koya, har muka gano cewa Nipprimmune’ zai iya maganin cutar korona.” Inji Adigwe.
“A wancan lokacin fa mun rika karade gidajen talbijin daban-daban, mu na sanar da abin da muka binciko, tare da rokon masu tallafawa su shigo ciki a yi hadin guiwar sa kudade domin mu karasa abin da ya rage kafin mu kai gacin tabbatar da maganin, har ya wadata yadda za a rika amfani da shi.”