• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    GARGAƊI GA BUHARI: ‘Ƙaƙudubar ƙarancin kuɗi na yi wa zaɓen 2023 da dimokraɗiyya babbar barazana’ – Akeredolu

    Gwamnatin Jihar Ondo ta faɗi dalilin da ya sa ba za ta buɗe masallacin cikin watan Ramadan ba

    Kotu ta yi wa gwamnatin Gombe da ‘yan sanda katanga da dan jarida, Dahiru Kera

    Kotu ta yi wa gwamnatin Gombe da ‘yan sanda katanga da dan jarida, Dahiru Kera

    Samuel Ortom

    Gwamna Ortom ya janye ƙarar da ya maka hadimin sa, wanda ya kayar da shi a zaɓen Sanatan Benuwai, kuma ya roƙi yafiya

    An kara wa ma’aikatan jinya na jihar Yobe albashi

    Akalla mutum 7,806 suka kamu da cutar tarin fuka a tsakanin shekarar 2021 – 2022 a jihar Bauchi

    Iyorchia Ayu ba alheri ba ne, baƙin jinin sa ne ya janyo faɗuwar PDP zaɓen 2023 – Chimaroke Nnamani

    Iyorchia Ayu ba alheri ba ne, baƙin jinin sa ne ya janyo faɗuwar PDP zaɓen 2023 – Chimaroke Nnamani

    Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu

    Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu

    Kashim Shettima of Borno

    SHARI’AR ZARGIN SHETTIMA YA FITO TAKARA WURI BIYU: Kotu ta kori ƙarar da PDP ta nemi a soke takarar Tinubu da Shettima

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    GARGAƊI GA BUHARI: ‘Ƙaƙudubar ƙarancin kuɗi na yi wa zaɓen 2023 da dimokraɗiyya babbar barazana’ – Akeredolu

    Gwamnatin Jihar Ondo ta faɗi dalilin da ya sa ba za ta buɗe masallacin cikin watan Ramadan ba

    Kotu ta yi wa gwamnatin Gombe da ‘yan sanda katanga da dan jarida, Dahiru Kera

    Kotu ta yi wa gwamnatin Gombe da ‘yan sanda katanga da dan jarida, Dahiru Kera

    Samuel Ortom

    Gwamna Ortom ya janye ƙarar da ya maka hadimin sa, wanda ya kayar da shi a zaɓen Sanatan Benuwai, kuma ya roƙi yafiya

    An kara wa ma’aikatan jinya na jihar Yobe albashi

    Akalla mutum 7,806 suka kamu da cutar tarin fuka a tsakanin shekarar 2021 – 2022 a jihar Bauchi

    Iyorchia Ayu ba alheri ba ne, baƙin jinin sa ne ya janyo faɗuwar PDP zaɓen 2023 – Chimaroke Nnamani

    Iyorchia Ayu ba alheri ba ne, baƙin jinin sa ne ya janyo faɗuwar PDP zaɓen 2023 – Chimaroke Nnamani

    Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu

    Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu

    Kashim Shettima of Borno

    SHARI’AR ZARGIN SHETTIMA YA FITO TAKARA WURI BIYU: Kotu ta kori ƙarar da PDP ta nemi a soke takarar Tinubu da Shettima

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

KORAR MAKIYAYA: Dattawan Yarabawa da Dattawan Arewa sun fara zare wa juna idanu

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
January 21, 2021
in Rahotanni
0
KORAR MAKIYAYA: Dattawan Yarabawa da Dattawan Arewa sun fara zare wa juna idanu

Wa’adin ficewa daga dazukan Jihar Ondo cikin kwanaki bakwai da Gwamna Rotimi Akeredolu ya bai wa Fulani makiyaya, ya fara tayar a kura tsakanin Kungiyar Dattawa Yarabawa Zalla (YCE) da kuma Kungiyar Dattawan Arewa (NEF)

Yayin da Kungiyar Dattawa Yarabawa Zalla ke goyon bayan Gwamna Akeredolu, su kuma Kungiyar Dattawan Arewa sun yi kira ga duk wani Bafulatani makiyayi da ke cikin dazukan jihar Ondo, ya yi zaman lafiya da jama’a. amma kuma kada ya sake ya tashi.

Kungiyar ta Dattawan Arewa ta ce duk wani makiyayin da ke zaune lafiya da jama’a ya yi zaman sa, kada wata barazana ta tayar masa da hankalin har ya yi tunanin tashi.

Tuni Ya Kamata A Kori Fulani Makiyaya – Dattawan Yarabawa

Ita dai Kungiyar Dattawa Yarabawa Zalla (Yoruba Elders Forum), ta ce ai tuni ne ma ya kamata a ce an fatattaki Fulani makiyaya daga cikin dazukan-gwamnatin jihar Ondo din.

Cikin wani jawabi da YEF ta fitar bisa sa hannun Babban Sakataren YEF, Kunle Olajide, ya ce tuni ya kamata a ce an fatattaki makiyayan, “saboda ai babu wata doka a Najeriya da ta ce wani daga wata jihar na da dama shiga wata jiha ya mamaye masu kasa, ya rika lalata masu amfanin gona ya na tayar da fitina, kuma jama’ar yanki su yi tsaye su na kallon sa.

“Dajin nan Dajin-gwamnati ne, amma kuma tun cikin 2015 makiyaya sun mamaye shi, su na lalata mana amfanin gona, su na kashe mana mutanen mu. Su na yi wa mata fyade. Kuma su na yin garkuwa da mutane, ana kai masu kudin fansa.

“Amma kuma abin takaici gwamnatin tarayya da jami’an tsaro sun kauda kai, sun toshe kunnuwan su daga kukan da mu ke yi masu.”

Dattawan sun nuna goyon gaya 100 bisa 100 ga Gwamna Akeredolu na korar makiyaya.

Kada Wani Makiyayin Da Ya Fice Daga Jihar Ondo –Dattawan Arewa

Sai dai kuma kakakin yada labarai na Kungiyar Dattawan Arewa, Hakeem Baba-Ahmed, ya yi kira ga Fulani Makiyaya da ke zaune Jihar Ondo cewa kowa ya yi zaman sa lafiya. Amma kada wanda ya fice daga jihar. “Kungiyar Dattawan Arewa na cike da mamakin rahoton da aka watsa cewa Gwamna Rotimi Akeredolu ya bai wa makiyaya wa’adin ficewa daga jihar Ondo. Yaya mutumin da ya kai matakin SAN a shari’a zai yi wannan kasassabar, ya kori mutanen da ke zaune wata jiha tsawon shekara da shekaru.” Inji Dattawan Arewa.

“Ai babu wani dan Najeriya da ke da ikon korar wani dan Najeriya daga wani wurin da ya ke zaune. Don haka kungiyar mu na ganin matakin da gwamnan ya dauka, zai iya tunzira jama’a kuma ba zai haifi da mai idanu biyu ba.”

“Idan akwai masu laifi accikin Fulanin, to alhakin gwamna ne ya dauki matakin duk da ya dace a zakulo su a hukunta su. Kuma babu inda Fulani ke da wata dokar kariyar kin fuskantar sharia’a idan sun yi laifi a Najeriya.”

PREMIUM TIMES ta buga labarin yadda Akeredolu ya maida wa Fadar Buhari martani cewa ta fi tausayin Fulani makiyaya fiye da sauran ’yan Najeriya –Jihar Ondo

Gwamnatin Jihar Ondo ta maida wa Fadar Shugaba Muhammadu Buhari raddi, dangane da yadda fadar ta yi kakkausan suka ga jihar Ondo, don ta bada wa’adin kwanaki bakwai ga Fulani makiyaya da ke cikin dazukan-gwamnatin jihar cewa su fice daga ciki.

Kamishinan Yada Labarai na Jihar Ondo, Donald Ojogo, ya bayyana cewa martanin da Kakakin Fadar Shugaban Kasa, Garba Shehu ya yi a Ondo, ya fi kama da cea fadar ta fi nuna tausayi ga Fulani makiyaya fiye da ko a kasar nan.

“Furucin Garba Shehu ya nuna inda fadar gamnatin tarayya ta fi nuna tausayi. Hakan dai babbar barazana ce ga dorewar zamantakewar jama’ar kasar nan a wuri daya.” Inji Ogoja.

“Mu na neman karin bayani daga gamnatin tarayya a yi mana dalla-dalla shin ko rashin mutuncin da masu fakewa da kiwo ke yi su na garkuwa da mutane, ko sun dogara ne da jingina ga bangon masu mulkin da su ke takama ne? Gaskiya ana yi a hakin kankasar nan barazana.”

Tankiyar ta samo asali tun daga ranar Litinin, bayan Gwamna Rotimi Akeredolu ya haramta wa makiyaya kiwo a cikin dajin-gwamnatin jihar Ondo.

A martanin Fadar Shugaban Kasa, Garba Shehu ya bai kamata a tauye wa makiyayan hakkin su na kiwo ba. Kamata ya yi a zauna a sasanta, a fitar da baragurbi daga cikin su.

Gwamnatin Jihar Ondo ta maida martani kamar haka:

“Abin tambaya a nan, shin wai wadannan makiyaya masu kashe mutane su na garkuwa su na fashi da makami, sun fi sauran jama’a da ita kan ta Gwamnatin Tarayya muhimmanci ne?

“Kuskure ne mutum ya fake cikin fadar shugaban kasa ya na fitar da maitar sa ta kabilanci a fili.”

PREMIUM TIMES ta tuntubi Ogoja a ranar Laraba inda ya tabbatar mata cewa ya yi wannan bayani.

Sannan kuma ya ce wa’adin da aka ba makiyayan na nan, ba za a fasa fatattakar su ba.

PREMIUM TIMES HAUSA ta bada labarin yadda Gwamnatin Ondo ta fatattaki Fulani makiyaya daga dazukan Jihar, tare da tukuicin tsauraran dokoki shida.

Gwamnan Jihar Ondo Rotimi Akeredolu, ya umarci dukkan wasu Fulani makiyaya da ke zaune cikin dazukan jihar (forest reserves), su fice daga cikin dajin nan da kwanaki bakwai.

Umarnin ko kuma dokar ya fara aiki ne daga ranar Litinin 18 Ga Janairu, 2021.

Akeredolu ya bada wannan umarnin ne a lokacin da ya yi ganawa tare da shugabannin Fulani makiyaya da kuma shugabannin kabilar Ebira da ke jihar.

Taron ya gudana a Babban Dakin Taro na Cocoa Conference Hall da ke cikin Gidan Gwamnatin Jihar Ondo a Akure, babban birnin jihar.

Akeredolu ya ce an dade ana fama da hare-hare da garkuwa da mutane wadanda wasu batagari ke yi da fakewa da kiwo amma su na garkuwa da mutane a jihar.

“A yau mun dauki babban matakin farko na dakile garkuwa da mutane da saukar manyan laifukan da ake aikatawa a fadin jihar nan.”

“Yawancin wadannan ayyukan garkuwa da mutane wasu batagari ne ke yin su masu fakewa da sunan makiyaya. Sun maida dazukan gwamnati wata mabuyar masu garkuwa da mutane, su na karbar makudan kudaden diyya.

“A matsayi na na Gwamnan Jiha wanda nauyin kare hakkin rayuka da dukiyoyin jama’a ke hannun sa, ina sanar da bijiro da wadannan ka’idojin da gaggawa, wadanda su ka hada da:

Tsauraran Dokoki 6 Da Gwamnatin Ondo Ta Kakaba Wa Makiyaya:

1. Makiyaya su gaggauta ficewa daga dukkan dazukan gwamnati da ke cikin jihar Ondo, nan da kwanaki bakwai, daga ranar Litinin 18 Ga Janairu, 2021 za su fara kirgawa.

2. An haramta kiwo cikin dare, saboda yawancin gonakin da makiyaya ke cinye wa amfanin gona, duk da dare ake yin aika-aikar.

3. An haramta zirga-zirgar shanun kiwo a kan manyan titina da kuma cikin gari.

4. An haramta kiwo ga duk wani yaron da ba balagi ba.

5. An umarci dukkan jami’an tsaron da ke Jihar Ondo su tirsasa bin wannan dokar tilas.

6. Amma gwamnatin mu mai tausayi ce, don haka duk wani mai son yin kiwo a jihar nan, to ya gaggauta yin rajista da hukumar da nauyin kula a kiwo ke kan ta.

Tags: AbujaFulaniMakiyayaNewsPREMIUM TIMESYarabawa
Previous Post

Gwamnati ta damu ganin yadda rahoto ya nuna yawan ragabza, bushasha da rashin iya aiki a hukumomin gwamnati

Next Post

INEC ta sanar da ranar zaben Gwamnan Jihar Anambra

Next Post
Independent National Electoral Commission (INEC) Chairman, Prof. Mahmood Yakubu, addressing a stakeholders meeting on 2019 General Elections’ postponement, in Abuja on Saturday (16/2/19).

INEC ta sanar da ranar zaben Gwamnan Jihar Anambra

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Jihar Ondo ta faɗi dalilin da ya sa ba za ta buɗe masallacin cikin watan Ramadan ba
  • PDP ta janye dakatarwar da ta yi wa Anyim, Shema, Fayose, ta fasa gurfanar da Gwamna Ortom gaban Kwamitin Ladabtarwa
  • Ƙungiyar Lauyoyin Najeriya ta ce a riƙa watsa zaman sauraren ƙarar da Atiku da Obi su ka maka Tinubu a talbijin kai-tsaye
  • ZAFIN FADUWA: Dalilin da ya sa aka turo sojoji don a murde zaben gwamnan Zamfara, PDP ta yi nasara – Matawalle
  • Bashin da ake bin Najeriya ya mirgina cikin ramin naira tiriliyan 46.25 kafin shiga 2023 – DMO

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.