Shugaba Muhammadu Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa wasikar neman amincewar su da sunayen manyan hafsoshin sojoji hudu da ya nada matsayin Shugabannin Tsaron Kasa.
Ya nada su a ranar Talata, jim kadan bayan sauke su Janar Buratai a ranar.
PREMIUM TIMES ta buga labarin cewa Buhari ya tsige Buratai da sauran Manyan Hafsoshin Tsaro, ya nada sabb
Shugaba Muhammadu Buhari ya amince da takardar sanarwar ajiye aiki da Manyan Hafsoshin Tsaron Kasa su hudu su ka yi.
Wadanda su ka ajiye aikin sun hada da Hafsan Hafsoshin Sojoji, Tukur Buratai, Babban Hafsan Tsaron Kasa, Janar Abayomi Olonisakin, Babban Hafsan Sojojin Ruwa, Vice Admiral Ibok Ibas da kuma Air Marshal Sadique Abubakar, Babban Hafsan Sojojin Sama.
Wata sanarwa da Kakakin Yada Labarai na Shugaba Buhari, Femi Adesina ya wallafa a shafin sa na Facebook, ta ce Buhari ya yi wa hafsoshin fatan alheri a dukkan al’amurran da su ka sa gaba bayan ritayar da su ka yi.
An maye guradun su da Manjo Janar Leo Irabor, matsayin Babban Hafsan Tsaron Kasa, Manjo Janar I Attahiru, matsayin Babban Hafsan Sojoji wanda ya canji Buratai, Rear Admiral A.Z Gambo, Babban Hafsan sojojin Ruwa, sai kuma Air-Vice Marchal I.O Amao, Babban Hafsan Sojojin Sama.
Buhari ya taya sabbin manyan hafsoshin kasar da ya nada murna, kuma ya yi horo gare su su kasance masu biyayya da aiki tukuru kan ayyukan da aka dora wa kowanen su.
Cikin wata sanarwa da Mashawarcin Musamman A Fannin Majalisar Dattawa, Babajide Omoworare, ya ce Buhari ya aika da wasikar ga Shugaban Majalisar Dattawa tun a ranar 27 Ga Janairu.
Ya ce an yi haka kamar yadda Sashe na 18 (1) na Dokar Aikin Soja ta Najeriya ta tanadar.
Ya ce ba gaskiya ba ne da ake cewa an nada su ba tare da an sanar da Majalisar Dattawa ba.
Discussion about this post