Hukumar NCDC ta sanar da karin mutum 281 da suka kamu da cutar Korona a Najeriya ranar Talata.
Alkaluman da hukumar NCDC ta fitar ranar Talata sun nuna cewa Legas ta samu karin mutum –123, FCT-64, Kaduna-38, Imo-15, Rivers-11, Filato-8, Ogun-5, Bayelsa-4, Kwara-4, Bauchi-3, Edo-3, Kano-2 da Osun-1
Yanzu mutum 67,838 suka kamu da cutar a Najeriya, mutum 63,430 sun warke, 1,176 sun rasu. Sannan kuma zuwa yanzu mutum 3,232 ke dauke da cutar a Najeriya.
Har yanzu dai jihar Legas ne ke da mafi yawan wadanda suka kamu da mutum 23,410, FCT –6,868, Oyo – 3,728, Edo –2,699, Delta –1,824, Rivers 2,996, Kano –1,795, Ogun –2,228, Kaduna –3,136, Katsina -1,030, Ondo –1,728, Borno –745, Gombe – 938, Bauchi –773, Ebonyi –1,055, Filato -3,877, Enugu – 1,332, Abia – 926, Imo –677, Jigawa – 331, Kwara –1,106, Bayelsa – 454, Nasarawa – 493, Osun –947, Sokoto – 166, Niger – 298, Akwa Ibom – 339, Benue – 496, Adamawa – 261, Anambra – 282, Kebbi – 93, Zamfara – 79, Yobe – 100, Ekiti – 365, Taraba- 163, Kogi – 5, da Cross Rivers – 90.
Domin samun ingantattun bayanai game da korona a Najeriya gwamnati tare da hadin guiwar UNICEF sun samar da wata layin kira na waya da za a rika samun labarin gaskiya game da cutar.
Mutum zai aika da sakon ‘Coronavirus’ zuwa lambar 24453, daga nan za a aiko masa da sakonni game da cutar da matsayin da duniya ke ciki da kasa Najeriya.
Domin shiga wannan dandali a facebook ko Kuma WhatsApp za a iya aikawa da sakon ‘Coronavirus’ zuwa ga +234 908 740 1607. Ko Kuma ta adireshin U-Report kamar haka @ureportnigeria.
Wakilin asusun UNICEF a Najeriya Peter Hawkins ya gargadi mutane da su cigaba da kiyaye sharuddan guje wa kamuwa da cutar korona cewa yin haka ne kadai mutum zai iya samun kariya daga corona.
Discussion about this post