• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

In Dai Har Irin Su Abdullahi Abbas Sune Shugabanni A Kano Da Arewa…! Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
December 23, 2020
in Ra'ayi
0
In Dai Har Irin Su Abdullahi Abbas Sune Shugabanni A Kano Da Arewa…! Daga Imam Murtadha Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai!

Assalamu Alaikum

Inna lillahi wa inna ilaihi raaji’uun! Inna lillahi wa inna ilaihi raaji’uun!! Inna lillahi wa inna ilaihi raaji’uun!!!

‘Yan uwa na masu daraja, wallahi, Allah ya sani, kuma shine shaida, tun da na kalli wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen yada labarai na zamani, wato soshiyal midiya, na shugaban jam’iyyar APC mai mulki a jihar Kano, wato Abdullahi Abbas, kawai sai na rude, hankalina ya tashi, na shiga damuwar da ban taba shiga irin ta ba! Ace wai wannan mutum shugaba ne a arewa, ace wannan mutum magidanci ne, da yake da iyali, mata, da yara!!

Abdullahi Abbas ya fito yana ashar, da zagi, da tsinuwa, da la’ana, da zuga ‘ya ‘yan mutane suyi tashin hankali, su kashe mutane, su zubar da jini, duk da sunan adawar siyasa tsakanin APC da PDP. Sun lalata yaran talakawa, sun mayar da su mashaya, sun mayar da su ‘yan daba, sun mayar da su ‘yan ta’adda, amma su sun boye nasu yaran, suna ta basu ilimi. Idan sun wuce kuma yaran nasu sune za suci gaba da jagorantar wadannan yara, ‘ya ‘yan talakawa, da suka lalata wa rayuwa.

Nayi imani da Allah, wannan bidiyo da ke yawo, mutane da dama sun gan shi, amma da yake wannan mutum dan jam’iyyah mai ci ne, dan gata ne, babu abunda za’ayi, kuma babu wani matakin da za’a dauka!

Kullun mu ‘yan arewa, muna ta yaudaran kawunan mu, muna ta munafuntar kawunan mu, muna ta surutan banza, muna ta yin taruruka na shan shayi a watse, muna ta yin tarukan karawa juna sani na karya, muna ta koke-koke da munafunce-munafunce, muna ta yin rubuce-rubuce na neman mafita, da kuma kokarin magance ko kuma kawo karshen matsalar tsaro da ta addabi yankin mu, amma duk mun manta cewa, mun fa bar jaki ne muna ta dukan taiki!

Dalilina na fadar wannan magana shine, to ta yaya zamu tsaya, muna munafuntar kawunanmu, munyi shiru akan kazaman ‘yan siyasar da ke lalata rayuwar matasanmu, sun mayar da su ‘yan daba, sun mayar da su ‘yan ta’adda, sun mayar da su marasa imani, marasa kishin addininsu, marasa kishin al’ummarsu, marasa kishin kasarsu, marasa kishin yankinsu, marasa kishin manyansu, marasa kishin na gaba da su da iyayensu? Na rantse da Allah, wanda babu abun bautawa da gaskiya sai shi kadai, ina mai shaida maku cewa, idan bamu fara daukar mummunan mataki akan irin wadannan ‘yan siyasar ba, idan bamu fara yin maganinsu ba, idan bamu fara nuna masu cewa da gaske muke yi ba, to wallahi babu yadda za’a yi mu iya magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin mu!

Yanzu domin Allah, shi wannan mutum, wato Abdullahi Abbas, da ya tara ‘ya ‘yan talakawa, miskinai, yana yi masu irin wannan mummunar lakca, don Allah ina nasa ‘ya ‘yan suke ne? Don girman Allah zai iya tara ‘ya ‘yansa ya isar masu da irin wannan sako, domin su tafi su aiwatar da shi akan wasu? Shin domin Allah irin yadda yake zuga wadannan matasa suyi ta’addanci, zai so nasa yaran su zama ‘yan ta’adda? Me yasa har kullun ake ta cutar da mu, ake ta cutar da matasan mu na arewa, ake ta mayar da mu baya, da sunan siyasa ko da sunan adawar siyasa, amma mun yi shiru, bamu cewa komai? Ga abubuwan da ke jawo muna rikice-rikice da tashin hankali da zubar da jini da rashin zama lafiya, kai da dukkanin matsalolin rashin tsaro, amma saboda munafunci irin namu, mun yi shiru, bamu cewa komai, sai kace wadannan wawayen kazaman ‘yan siyasar sun fi karfin mu ko sun fi karfin kowa?! Kuma don rashin sanin ciwon kai, idan wani ya fito yayi magana, ya fadakar, ya jawo hankalin hukumomi da manya, amma sai ka ga wani wawa shi kuma can, wai yana cewa baka kyauta ba, ai ba haka ya kamata kayi ba!

Shi mai wannan irin magana, yana fada maka ita ne, saboda ba’a saci dan uwansa ko ‘yar uwarsa ba, ko ba’a saci dan sa ko ‘yar sa ba, ko kuma ba’a yiwa uwarsa ko ‘yar sa ko matar sa fyade yana kallo ba, shi yasa yake wannan magana!

Don Allah, don Allah, don Allah ina jami’an tsaron Najeriya suke ne? Don Allah, don Allah, don Allah ina shugaban kasa Muhammadu Buhari yake ne? Don Allah, don Allah, don Allah ina gwamnonin mu na arewa suke ne? Don Allah, don Allah, don Allah ina dukkanin manyan jihar Kano suke ne, da matasan jihar Kano, da manyan arewa da matasan arewa da malaman arewa da sarakunan arewa, kai da duk wani mai fada aji a arewa, ina kuke ne don girman Allah, a lokacin da wannan mutum, Abdullahi Abbas yake wadannan maganganu? Shin kuna nufin ku fada mani cewa yanzu yankin mu na arewa mai albarka ya zama wurin da ko wane irin wawan mutum zai fito yayi abunda ya ga dama, ya fadi maganganun da yaga dama, wadanda zasu iya zama sandiyyar tarwatse arewa, ba tare da an taka masa burki ba? Ba tare da an dakatar da shi ba? Ba tare da an dauki mataki a kan sa ba? Ina mai tunatar da ku cewa fa, wallahi irin wannan yin shiru akan lamurra da muke yi, tare da kyale kowa yayi abunda ya ga dama, da nuna halin ko-in-kula, shine ya kai mu halin da muke ciki a yau. Ya kamata mu san wannan!

Ya ku manyan arewa, ku sani, wallahi muna matukar ganin girman ku, tare da baku daraja, da son ku da kaunar ku, a matsayinku na manyanmu kuma iyayenmu, shi yasa bamu daukar doka a hannun mu game da irin wadannan al’amurra. Sannan kuma mun san cewa dokar kasar mu bata yarda mutum ya dauki doka a hannunsa ba, kasancewar akwai hukuma. Amma idan har kun kasa, kuma hukuma za ta bamu goyon baya tare da izini, to wallahi ina mai tabbatar maku cewa mu a shirye muke da muyi maganin duk wani shedani, dan ta’adda, da ikon Allah kuma da buwayarsa! Kuma a shirye muke da mu yi maganin duk wasu wawaye, kazaman ‘yan siyasar da ke lalata muna rayuwa, kuma su lalata rayukan matasanmu, alhali su ba zasu taba yarda ‘ya ‘yansu suyi irin abun da suke zuga ‘ya ‘yan wasu suyi ba!

Kuma wannan magana da nike fada, kar wani ya dauka da wasa nike yi, ko kuma ba’a nike yi. Ina mai rantsuwa da Allah da gaske nike yi, kuma babu wasa ko ba’a a cikin ta!

Ya kamata jama’ah su fahimci cewa fa mungaji, mungaji, mungaji da irin wannan cin mutunci da ake yi muna, da irin wannan wulakanci da ake yi muna. Ya isa haka nan!

Kullun muna ce maku ya kamata mutanen kirki, na kwarai su shiga siyasar nan, domin idan basu yi ba, to mutanen banza, ‘yan tasha, marasa da’a da kishi da tarbiyyah, sune zasu shige ta, su mamaye komai, kuma su zama shugabannin ku. To yanzu ga irin ta nan, wannan shine muke ji maku tsoro, ga shi nan ‘yan iska, ‘ya ‘yan banza, suna kusa ga su mamaye siyasar. Kuma da an wayi gari duk sune shugabannin ku, to wallahi kun shiga uku, kun lalace!

Saboda haka ya zama dole, kuma wajibi mu shiga taitayinmu. Ni na riga na gaya maku, ba zamu taba rungume hannuwa, muna kallo ana cutar da yankin arewa da Najeriya ba muyi shiru. Da ikon Allah sai kowa ya gane na kwarai, sannan sai kowa ya gane mugu. Idan kuma muka gane su, to zamu ci gaba da bayyana maku cewa yanzu me ya kamata muyi da su da ikon Allah!

Wassalamu alaikum

Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad Gusau ne ya rubuta daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun Imam a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaHausaLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

GARABASAR KIRSIMETI: Gwamnati na sayar da kazar naira 5,000 a kan naira 1,800

Next Post

An tsiro da kamfen din goga wa Buhari kashin kaji – Fadar Shugaban Kasa

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
Dalilin da ya sa Buhari bai ce komai ba kan zargin kisan mutane a Lekki

An tsiro da kamfen din goga wa Buhari kashin kaji – Fadar Shugaban Kasa

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • HIMMA DAI MATA MANOMA: Rashin jari mai kauri ya sa noma na ya ƙi gaba, ya ƙi baya – Wata mace mai himma
  • CIRE TALLAFIN MAI: Kungiyoyin ma’aikatan lantarki, Ƴan jarida da na Kwadago za su tsunduma yajin aiki daga ranar Laraba
  • Yadda bashin Dala Miliyan 95 na Bankin Musulunci ya bunƙasa noma a ƙananan hukumomin Kano 44 – Hamisu, Kodinetan KSADP
  • Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati
  • Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.