• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

HARKALLAR MALABU: Kotu ta hana Gwamnatin Najeriya taka wa Mohammed Abacha birkin hana shi shiga kotu

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
December 24, 2020
in Babban Labari
0
HARKALLAR MALABU: Kotu ta hana Gwamnatin Najeriya taka wa Mohammed Abacha birkin hana shi shiga kotu

Babbar Kotun Tarayya da ka Abuja ta ki amincewa da bukatar Gwamanatin Najeriya domin haka Mohammed Abacha shigar da kara, inda ya yi ikirarin cewa rigiyar danyen man fetur mai lasisi OPL 245, ta sa ce, halak malak.

Shi dai Mohammed Abacha ya maka Gwamnatin Tarayya kotu, tare da kamfanin Shell Exploration anda Production Ltd da kuma Nigeria Agip Exploration Company, dukkan su kamfanonin da ke hako danyen mai a Najeriya.

Ita dai gwamnatin tarayya ta yi kokarin hana Mohammed,dan tsohon Shugaba na mulkin soja ikirarin mallakar rijiyar danyen man, mai lamba 245.

Sauran wadanda Mohammed Abacha ya maka kotu, sun hada da Ministan Harkokin Fetur, Shell Nigeria Ultra-Deep Ltd da kuma tsohon ministan fetur, Dan Etete.

Mohammed Abacha ya shigar da kara mai lamba FHC/ABJ/201/2017, inda ya ke ikirarin cewa ai shi ne ya fi kowa hannun jari mai kauri a rijiyar danyen mai ta Malabu Oil and Gas Ltd.

A hukuncin da ta zartas, Mai Shari’a Binta Nyako ta ce kotu na da ‘yancin tsayawa ta saurari karar da Mohammed Abacha ya shigar wadda ke da nasaba da danyen man fetur da gas.

Binta ta ce Gwamnatin Najeriya da sauran wadanda Mohammed Abacha yam aka kotu, ba su da ikon hana kotu sauraren karar da dan na marigayi Abacha ya shigar.

Sannan ta ce Mohammed Abacha na da ikon hadawa da Ministan Harkokin Mai na Najeriya na yanzu duk ya maka kotu kamar yadda ya yi, domin a bisa doka, za a iya maka shi kotu, shi ma kuma zai iya maka wani kotu idan ta kama.

MALABU OPL 245: Rijiyar Da Ta Fi Kowace Rijiya Yawan Danyen Mai Afrika:

Ita wannan rijiya, wadda ke da lasisi mai lamba OPL 245, an kiyasta cewa ta fi kowace rijiyar danyen mai zurfi da yawan ruwan mai kwance a karkashin kasa.

An kiyasta akwai danyen mai kwance a karkashin ta fiye da ganga bilyan tara (9). Ministan Fetur Dan Etete ne ya bayar da lasisin mallakar rijiyar ga kamfanin Malabu, a cikin 1988, a lokacin Etete din ne Minista.

A lokacin Mohammed Abacha ne ke da kashi 50 bisa 100 na jarin kamfanin amma ta hannun sunan bogi, na wani Kwekwu Amafegha, wanda bagaraswa ce, babu wani mai sunan.

Daga baya sai Etete ya yi ikirarin cewa ai shi ne ya mallaki kamfanin na Malabu, domin hukumar gudanarwar kamfanin sun mallaka masa shi.

Sai dai Mohammed Abacha ya karyata Etete, ya ce karya ya ke yi, babu lokacin da aka yi wannan yarjejeniyar.

An dai bayar da rijiyar mai lamba 245 a zamanin mulkin Sani Abacha. Shi kuma Etete ya yi ikirarin mallakar rijiyar bayan mutuwar Abacha.

Mohammed Abacha kuma a yanzu ya ce har yanzu shi ke da kashi 50 bisa 100 na jarin kamfanin na Malabu, wanda babu mai yawan jari a ciki kamar sa.

Markabun OPL 245 Cikin 2011:

An sayar da rijiyar mai lamba OPL 245 ga kamfanin Shell da Eni cikin 2011. An biya dala bilyan 1.1, amma fiye da rabin kudaden su ka shiga aljihun Dan Etete, aka yi ta jidar kudaden ana bayarwa cin hanci ga jami’an gwamnatin Najeriya da na Shell da Eni.

Wannan harkalla ta janyo an yi ta kwatagwamgwamar shari’a a Ingila, Najeriya da kuma Italiya.

Mai Shari’a Binta Nyako ta aza ranar 9 Ga Maris, 2021 fara shari’a.

Gada-gada Da Harkallar Cinikin Rijiyar Malabu Oil 245

HARKALLAR MALABU: AA Oil, da ya karbi dala miliyan 520 ya gurfana a kotun Italiya

Wani dan gada-gada mai suna Abubakar Aliyu, ya gurfana a gaban wata kotun kasar Italiya da ke burnin Milan.

An ce Aliyu shi ne ya rika zama wani gogarman gada-gadar wasu manyan jami’an gwamnatin Goodluck Jonathan suka rika amfani da shi ya na karbar musu makudan milyoyin daloli.

Kotu na ci gaba da sheka masa ruwan tambayoyi dangane yadda aka karkatar da dala biliyan 1.1 daga kamfanin harkar main a Shell da Eni, harkallar da aka ce a tarihin hada-hadar mai ba a taba yin kamar ta ba a fadin Afrika.

MA’ANAR HARKALLAR MALABU: Ita ce wata karimtsa-da-rimatson cuwa-cuwar zunzurutun kudade har dala bilyan 1.1 da kamfanonin hakar danyen main a Shell da Eni suka yi, tare da hannu da hadin bakin yin amfani da asusun ajiyar kudaden gwamnatin tarayyar Najeriya da dama.

An yi wannan karimtsa-da-rimatso ne a lokacin da Dan Etete ya na Ministan Harkokin Man Fetur na Najeriya. Kuma an tabbatar da cewa ba a taba yin harbat-ta-Matin harkalla kamar wannan ba a kamfanin Shell da Eni a fadin Afrika.

Daga cikin wasu asusun ajiya wanda Dan Etete ne kadai ke da hannu da ikon cirar ko da kwandala daga ciki ne aka rika rorar kudade ana zurarawa cikin asusun ajiyar kudi na dan gaga-gada Abubakar Aliyu, wanda aka fi sani da AA Oil.

AA Oil shi ne ke da wani katafarfen gida mai kallon otal din Hilton a Abuja. Gidan ya na kuma jikin farkon titin Gana Street da ke Maitama, Abuja. Ya na daya daga cikin kantama-kantaman gidajen alfarma a Abuja.

KARIMTSA-DA-RIMATSO

An ce an zurara har Dala milyan 520 cikin asusun sa.

Fadi-tashin binciken da aka rika yi ne aka gano cewa AA Oil fa gada-gada ce ya ke yi wa wasu jami’an gwamnati, ba harkar gaban kan sa ba ce.

A cikin 2011 ne Goodluck Jonathan ya bada iznin ya cire kudaden a matsayin kudin biyar farashin Rijiyar Mai wadda ke da lamba OPL 245, daya daga cikin manyan rijiyoyin man da suka fi albarkar danyen mai kwance a karkashin su.

Da farko Shell da Eni sun nuna cewa su ba su ma san da wannan harkalla ba, ba su ci zomo ba, kuma ba a ba su ratayar ko da fatar zomo ba. Cewa suka yi ba su san kudaden a hannun Etete da ‘yan koren sa za su koma ba.

Sai dai kuma wasu hujjoji da PREMIUM TIMES ta mallaka, sun tabbatar cewa karya Shell da Eni ke yi, da su aka kaso zomo kuma da su aka gasa shi, sannan da su aka cinye naman sa.

A zaman yanzu da ana ci gaba da gurfanar da Shell, Eni, Etete, AA Oil da wasu jami’ai da dama a wata kotun Italy da ke birnin Milan.

A ci gaba da shari’ar da aka gudanar a yau Laraba da safe, masu gabatar da kara sun sanar wa Mai Shari’a cewa wani lauyan kasar Italy wanda ya ce shi ne lauyan Abubakar Aliyu mai AA Oil, ya kai musu ziyara jiya Talata inda ya tambayi a sake daga masa kafa domin a dan kara jinkirta shari’ar.

Amma kuma wani hamshakin lauya wanda ke aiki a Kamfanin Lauyoyin Barnaby Pace of UK Global Witness, wanda ya halarci zaman kotun ko a yau Laraba da safe, ya ce lauyan bai je kotu ba a yau, kuma bai aiko da dalilan rashin zuwan sa kotun ko da a rubuce ba.

KALLO YA KOMA KOTUN BIRNIN MILAN

Yayin da aka fara gabatar da bayanai a gaban mai shari’a, Aliyu ya tabbatar da cewa ya samu bayanan dukkan caje-cajen da ake yi masa.

Amma kuma ya ce shi zai iya kin amsa tuhume-tuhumen don kada gina wa kan sa rami kuma ya rufta da shi a gaban alkalin Italiya.

Sai dai kuma daga bayan PREMIUM TIMES ta samu tabbacin cewa lauyan da ke kare AA Oil ya halarci kotun a birnin Milan a yau Laraba.

Haka kuma ita ma gwamnatin Najeriya akwai lauyan da ta tura da ke sauraren ba’asin bayanai kuma ya ke bibiyar shari’ar a cikin kotun.

Aliyu AA Oil ya nemi a kara jinkirta masa lokaci, ta yadda sabbin lauyoyin sa za su yi nazarin yadda tuhume-tuhumen da ake yi masa suke, sannan kuma su san irin kamun ludayin da za su yi idan an fara sa-in-sa a gaban mai shari’a.

PREMIUM TIMES ta gano cewa masu gabatar da kara sai kwanan nan suka aika wa AA Oil sammacin tuhume-tuhumen da ake yi masa.

To a yau Laraba mai shari’a ya amince ya jinkirta wa Aliyu har zuwa lokacin da lauyoyin sa za su yi nazarin takardun tuhume-tuhumen da ake yi masa. Ya ce caje-cajen da ake yi masa masu nauyi ne matuka, su na da bukatar lauyoyin sa su je su yi nazari.

Mai Shari’a ya ce zai bayar da ranar da za a dawo a ci gaba da shari’a.

Da farko an jinkirta gurfanar da AA Oil a kotu ne, saboda jami’an EFCC a Najeriya sun ce shi da sauran wadanda ake zargi duk sun cika wandon su da iska, sun tsere.

Sai a cikin watan Maris, 2013 ne EFCC ta sake buga musu sabbin caje-caje, shi da sauran wasu, har da Mohammed Adoke, tsohon Ministan Shari’a na zamanin mulkin Goodluck Jonathan da ministan harkokin man fetur na lokacin, Dan Etete. An tuhume su da hannu wajen yi wa dalar Amurka bilyan daya da milyan dari daya kurbar ruwan shayi.

Duk da cewa Mohammed Adoke ya sha musanta cewa ba da shi aka ci kudin ba. Amma kuma tun da ya fice daga Najeriya, har yau ya ki dawowa domin ya amsa tuhumar da ake yi masa, ballantana ya kare kan sa.

Mai Shari’a ya ce zai bayar da ranar da za a dawo a ci gaba da shari’a.

Tags: AbujaHausaLabaraiMalabuNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Majalisar Kolin Harkokin Addinin Musulunci ta yi sabon Mataimakin Shugaba

Next Post

Kungiyar Miyetti Allah ta taya Kiristoci murnar Kirsimeti, ta yi kiran zaman lumana a tsakanin su

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
An zargi wasu makiyaya da kashe Sufeton ’Yan Sanda a Jihar

Kungiyar Miyetti Allah ta taya Kiristoci murnar Kirsimeti, ta yi kiran zaman lumana a tsakanin su

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Kada ku tausaya min don na faɗi zaɓen Sanatan Zamfara – Sanata Marafa
  • JIRAN TSAMMANI: Tinubu zai saka wa waɗanda su ka yi wa APC hidima da waɗanda su ka wahala saboda jam’iyya – Marafa
  • Uba Sani ya yi sabbin nade-nade 27, ya nada Sani Liman shugaban ma’aikatan fadar gwamnati
  • SHUGABANCIN MAJALISAR DATTAWA: ‘A saka min wahalar da na yi wa APC, a ba ni shugabancin Majalisar Dattawa’ – Osita Izunaso
  • SHUGABANCIN MAJALISA: ‘Ba zan janye wa kowa ba, amma na ‘jone’ da guruf ɗin Abdul’aziz Yari’ – Orji Kalu

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.