• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Shin Wanene Sarkin Zazzau Na 19, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli? Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
November 3, 2020
in Ra'ayi
0
Emir of Zazzau Ahmad Nuhu Bamalli

Emir of Zazzau Ahmad Nuhu Bamalli

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

Assalamu Alaikum

Ya ku jama’ah, sai mu kara yin godiya ga Allah Ta’ala, da ya kaddari masoyinmu, Ahmad Nuhu Bamalli shine ya zama Sarkin Zazzau na 19. Ina rokon Allah Ta’ala ya taya shi riko, ya dafa masa, kuma yasa masa hannu cikin wannan nauyi da jagoranci da ya dora masa, kuma ya kare shi, ya tsare shi daga jin kunyar duniya da ta lahira, ya kare shi daga dukkan makircin masu makirci, amin.

‘Yan uwa na masu daraja, ya kamata mu san wanene wannan sabon Sarki na Zazzau. Domin mu kara hakikancewa akan cewa lallai a yau Zaria da al’ummarta sun dace, kuma sun yi sa’ar nagartaccen Sarki, mai ilimi, kuma mai kaunar jama’arsa.

To shi dai Mai Martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli shine Sarki na 19 a jerin sarakunan masarautar Zazzau, kuma shine Sarki na farko daga gidan Mallawa da ya hau gadon Sarauta cikin shekaru 100, bayan rasuwar kakansa Sarki Malam Aliyu Dan Sidi a shekarar 1920.

Kuma Ahmad Nuhu Bamalli ya fito ne daga gidan Mallawa, sannan shine Magajin Garin Zazzau kafin naɗinsa Sarki a ranar Laraba, 7/10/2020.

Kuma Ambasada Ahmad ɗa ne ga Alhaji Nuhu Bamalli tsohon Magajin Garin Zazzau, kuma tsohon minista a Najeriya.

Kuma sabon Sarkin na Zazzau, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli masanin shari’a ne da diflomasiyyah, shine jakadan Najeriya a Thailand kafin ya zamo Sarki.

Saboda girman sarautarsa ta Magajin Garin Zazzau, da kirkinsa, da mutuncinsa, da haba-habarsa da jama’ah, da kuma kusancinsa da gwamnati yasa aka rinka sanya shi a jerin waɗanda ka iya zama sabon Sarkin Zazzau na 19.

An haifi Ahmad Nuhu Bamalli a birnin Zaria, ranar 8 ga watan Yuni na 1966.

Mahaifinsa, Alhaji Nuhu Bamalli, yana cikin mutanen da suka yi fafutukar samun ‘yancin kan Najeriya, kuma ya taba zama ministan harkokin wajen kasar, sannan ya rike sarautar Magajin Garin Zazzau, wadda dan nasa Alhaji Ahmad ya gada bayan rasuwarsa a 2001 (Ina rokon Allah ya gafarta masa, amin).

Sabon Sarkin na Zazzau, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli, yayi karatunsa na firamare da sakandare a garin Kaduna, sannan ya tafi Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria, inda yayi Digirinsa na farko a fannin aikin lauya a 1989.

Kazalika yayi Digirinsa na biyu (Masters) a fannin harkokin kasashen duniya da diflomasiyya a Jami’ar ta Ahmadu Bello a 2002.

Sannan Jami’o’in da ya halarta domin yin wasu kwasa-kwasai sun haɗa da Harvard da Oxford da Northwestern University da ke Chicago da kuma Jami’ar Pennsylvania da ke Amurka.

Ahmad Nuhu Bamalli yayi kusan ɗaukacin rayuwarsa ta aiki ne yana aiki a bankuna, inda kuma ya taɓa yin aiki a kamfanin da ke buga kudin Najeriya (Nigerian Security Printing and Minting).

A shekarar 2017 ne shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya naɗa shi a matsayin jakadan kasar a Thailand. Gabanin nan, ya taɓa riƙe muƙamin Kwamishinan Hukumar Zaɓe ta jihar Kaduna.

Sabon Sarkin na Zazzau yana da mata ɗaya, Mairo A. Bamalli da kuma ‘ya’ya biyar – namiji ɗaya da mata huɗu (Ina rokon Allah ya raya su, yasa masu albarka, amin).

• Muhimman abubuwan da ya kamata mu sani game da sabon Sarki a takaice:

1. An haifi Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli a shekarar 1966 a birnin Zaria, Najeriya.

2. Yayi karatun aikin lauya a digirinsa na farko daga jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria, a shekarar 1989. Digiri na biyu (masters) a harkokin kasashen waje da diplomasiyyah a dai duk jami’ar, shekarar 2002.

3. Kuma ya samu shaidar karatu ta Post Graduate Diploma akan gudanarwa, daga jami’ar kimiya da fasaha ta jihar Enugu, a shekarar 1988.

4. Yayi wani kwas akan sasanta rikice-rikice a jami’ar York da ke kasar Ingila, a 2009, kafin daga bisani ya wuce jami’ar Oxford da ke kasar Ingilar, in da ya samu takardar shaidar karatu ta Diploma a fannin jagoranci (organisational leadership), a shekarar 2015.

5. Sabon Sarkin na Zazzau, wato Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli, babban kwararre ne, wato Senior Fellow, wanda yake da kwarewa ta shekaru ashirin da shida a harkar banki, hulda da jama’ah, harkar sadarwa da kuma sarrafa kayayyaki.

6. Kuma shi tsohon dalibin shahararriyar makarantar nan ce ta koyon harkokin kasuwanci (Harvard Business School), a inda ya samu shaidar takardar karatu ta GMP, a 2011.

7. Sannan mukamin da ya rike kafin zamansa Sarkin Zazzau, wato Magajin Garin Zazzau, shine babban mukami na biyu a duk fadin masarautar Zazzau.

8. Yana zaune lafiya da iyalinsa, kuma cikin koshin lafiya. Yana auren Hajiya Mairo A. Bamalli, kuma suna da ‘ya ‘ya biyar, namiji daya mata hudu. Ina rokon Allah Ta’ala ya albarkace su, amin.

9. Sarkin Zazzau na 19, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli, kafin hawansa sarautar Zazzau mai daraja, shine ambasadan Najeriya a kasar Thailand, da kuma Republic of the Union of Myanmar.

10. Ya rike mukamin Kwamishinan hukumar zabe mai zaman kan ta na jihar Kaduna, tsakanin 2015 zuwa 2017.

11. Sabon Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli, ya taba rike mukamin Acting Managing Director/Chief Executive Officer and ED Corporate Services a Nigeria Security Printing and Minting Plc, tsakanin 2011 zuwa 2014.

12. Tsakanin shekarar 2007 zuwa 2009, ya taba rike mukamin Human Resources Manager a hukumar Nigerian Mobile Telecommunications Limited (MTEL).

13. Mai Martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli, ya taba rike mukamin Chairman, Board of Directors, na Tawada Limited, wanda wani yanki ne na Nigeria Security Printing and Minting plc, daga shekarar 2012 zuwa 2014.

14. Kuma shi member ne na Transition Committee na jihar Kaduna, a shekarar 2016.

15. Kuma Mai Martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli ya taba zama ma’aikaci a hukumar Abuja Metropolitan Management Agency.

16. Sannan uwa-uba, sabon Sarkin Zazzau na 19, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli, duniya ta shaida cewa, shi mutum ne mai gaskiya, mai rikon amana, mai hakuri, mai nuna jaruntaka da kwazo, da juriya, da jajircewa a cikin dukkanin al’amurransa; sannan shi mutum ne mai kishin addininsa, mai taimakon addini, mai taimakon al’ummah, mai tausayi, mai son talakawa, mai kaunar zaman lafiya, hadin kai da ci gaba; Shi mutum ne marar nuna banbanci ko kabilanci, shi mai kaunar jama’ah ne matuka, kuma mai kyauta, mai alkhairi. Sandiyyar haka nike shaidawa ‘yan uwana Zazzagawa, da dukkanin mutanen arewa, da ma Najeriya baki daya cewa, su sani, da yardar Allah, Mai Martaba Sarkin Zazzau Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli ba zai taba basu kunya ba! Da yardar Allah, sai an ji dadi, kuma sai an yi murna da zamansa Sarkin Zazzau. Sai ance gwamma da aka yi da yardar Allah, Mahaliccinmu.

Sannan ina kira, da roko, da lallashi ga dukkanin al’ummah, cewa, lallai ya zama wajibi, ya zama tilas, ya zama dole muci gaba da yiwa wannan bawan Allah, wato Mai Martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli, da sauran shugabannin mu, addu’a da rokon Allah yasa su gama lafiya, Allah ya kama hannayensu, yayi riko da hannayensu, ya dora su akan abun da yake daidai, wanda Allah yake so, kuma ya yarda da shi, amin thummah amin.

Daga karshe, muna nan muna ta addu’o’i da rokon Allah Ta’ala ya taya shi riko, amin. Da yardar Allah ba zamu gajiya ba akan wannan!

Wassalamu Alaikum,

Dan uwan ku: Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuta daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun Imam a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaAhmadBamalliHausaLabaraiNewsNuhuPREMIUM TIMES
Previous Post

KORONA: Mutum 137 suka kamu da cutar a Najeriya ranar Talata

Next Post

Gobara ta babbake gidaje 1,200 a jihar Barno

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
FIRE-OUTBREAK

Gobara ta babbake gidaje 1,200 a jihar Barno

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Abubuwa 12 Da Suka Hana A Ga Ƙoƙarin Mulkin Buhari
  • YUNƘURIN BALLEWA DAGA NAJERIYA: Yadda tsagerun Yarabawa suka kama Gidan Radiyon Gwamnatin Tarayya, kwana ɗaya kafin rantsar da Tinubu
  • RA’AYIN PREMIUM TIMES: Shekarun Mulkin Buhari: An sake ɓata goma, biyar ba ta gyaru ba
  • Zan yi tafiya da kowa da kowa a gwamnati na – Uba Sani
  • TINUBU: Abinci zai wadata cikin farashi mai sauƙi

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.