• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Kaɗan Daga Cikin Haƙkin Mata A Musulunci, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
November 15, 2020
in Ra'ayi
0
Woman In Hijab

Woman In Hijab

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

Assalamu Alaikum

Ya ku bayin Allah, ku sani, lallai addinin Musulunci ya bai wa mace wani irin nau’i na kulawa, ya bata matsayi da kariya, wanda ya sanya girmanta ya daukaka. Kuma Musulunci ya kebance ta da kyautata mu’amala, kasancewar ta na ‘ya, ko mata, ko ‘yar uwa, ko uwa, sai Musulunci ya tabbatar tun daga farko cewa lallai namiji da mace an halicce su ne daga asali guda daya, don haka a dan Adamtaka dukkanin su daya ne. Allah yana cewa:

“Ya ku mutane! Ku bi Ubangijin ku da takawa, Wanda Ya halitta ku daga rai guda, kuma Ya halitta, daga gare shi, ma’auransa, kuma Ya watsa daga gare su maza masu yawa da mata….” [Nisa’i: 1]

Akwai wasu ayoyin a wadansu wurare da suke bayyana binne ra’ayin kokarin banbantawa tsakanin tarayyar namiji da mace a cikin asalin dan Adamtaka. Gini akan wannan asali, da inkari akan al’adun jahiliyya, na al’umomin da suka gabata, yasa Manzon Allah (SAW) ya tashi tsaye kan batun bai wa mace kariya da kwato mata hakkinta da aka danne, har ya kai ta matsayin da bata taba samun kanta ba a ciki daga cikin al’umomin da suka gabata, ba’a kuma taba samu ba a cikin al’ummomin da suka zo daga baya, ta yadda Annabi ya sunnanta mata wasu hakkoki da suka kebance ta, wadanda a yau mata suke kokarin kwato irin su a turai, amma basu samu ba.

A wata magana mai cike da fasaha, wadda ke dauke da wata ka’ida mai muhimmanci, wadda Manzon Allah (SAW) ya bayyana, ta nuna cewa mata suna daidai da maza ta matsayi da girma da mutunci. Ba za’a tauye masu hakan ba saboda kasantuwarsu mata kawai. Manzon Allah (SAW) yace:

“Mata abokan (shakikan) maza ne.” [Tirmizi ne ya ruwaito]

Ma’ana kwatankwacin su ne.

Kuma ya tabbata cewa shi Manzon Allah (SAW) ya kasance mai yawan wasicci ne akan mata, har yana fadawa Sahabbansa cewa:

“Kuyi wasiccin alheri ga mata.” [Bukhari]

Irin wannan wasiyyah ta maimaitu daga bakin Annabi (SAW) a Hajjin bankwana, lokacin da yake magana da dubban Al’ummar shi. Don haka idan muka so yin bayanin abin da Manzon Allah (SAW) ya girka na turakun girman mace, da darajar ta, da daukakarta, zamu iya fahimtar hakan ne idan muka fahimci yanayin da ta tsinci kanta a lokacin Jahiliyyar da, da kuma jahiliyyar yanzu, domin ganin irin duffan da take rayuwa a ciki, da wannan ne zamu ga hakikanin halin da mace take ciki a rayuwar Musulunci. Kasantuwar a yau, ana kokarin mayar da mata ‘yan zanga-zanga a tituna, da sunan wayewa ko da sunan kwatar ‘yanci, ko da sunan yakar zalunci da azzalumai. Kasantuwar ayau, ana kokarin mayar da mata wasu kayan jin dadi kawai da holewa. Kasantuwar binne mata da ransu da ake yi, yana daga cikin mugayen dabi’un mutanen Jahiliyyah a da, sai Musulunci yazo da haramcin yin hakan, a inda Allah Madaukaki yake cewa:

“Kuma idan wadda aka binne ta da rai aka tambaye ta. Saboda wane laifi ne aka kashe ta?” [Suratut-Takwir, aya ta: 8-9]

Irin wannan danyen aiki, ya wayi gari daya daga cikin manyan laifuka, kamar yadda ibnu Mas’ud ya ruwaito cewa:

“Na tambayi Manzon Allah (SAW) cewa wane zunubi ne yafi girma?” Sai yace: “Ka sanya wa Allah kishiya alhali shine ya halicce ka.” Sai nace: “sai wane kuma?” Yace: “Ka kashe dan ka wai don tsoron talauci.” Sai nace sai wane?” Sai yace: “Ka yi zina da matar makwabcinka.” [Bukhari]

Manzon Allah (SAW) bai tsaya nan ba wurin bada kariya ga hakkin mata, sai da ya kwadaitar wurin kyautata masu a lokacin da suke kanana, yace:

“Duk wanda ya jibinci wani abu daga lamarin ‘ya’ya mata, sannan kuma ya kyautata masu, to zasu kasance sutura da kariya a gare shi daga azabar wuta.” [Bukhari]

Haka nan Manzon Allah (SAW) yayi umurni da a karantar da ‘ya mace, ya tsawatar cewa kar a yarda a bar ta cikin duhun jahilci, a inda yace:

“Duk mutumin da yake da ‘ya mace sai ya karantar da ita, kuma ya kyautata karantar da ita, ya tarbiyyantar da ita, kuma ya kyautata tarbiyyantar da ita, to yana da lada biyu.” [Bukhari]

Idan kuwa ta girma, ta zama budurwa, to Manzon Allah (SAW) ya ba ta ‘yancin ta zabi mijin da yayi mata ta aura, ta bar wanda bata so. Kuma ba ya halasta a tilasta mata ta auri wanda bata so, shi yasa Annabi (SAW) yace:

“Bazawara ita tafi cancanta da kanta sama da waliyyin ta, budurwa kuma ana neman izinin ta ne, izinin ta kuma shine shirun ta.”

Haka nan ya kara da cewa:

“Ba’a aurar da bazawara har sai an nemi umurnin ta, ba’a aurar da budurwa har sai an nemi izinin ta.” Sai suka ce: “Ya Manzon Allah, menene izinin ta?” Sai yace: “Shirun ta.” [Bukhari]

Idan ta zama matar aure kuma, sai Manzon Allah (SAW) ya kwadaitar wurin kyautata mata mu’amala da zamantakewa, yana mai bayyana cewa kyautata zamantakewa da mata, yana daga cikin hankalin namiji da karimcin shi. Annabi (SAW) ya fada cewa:

“Duk mijin da ya shayar da matarsa ruwa to zai samu lada.”

A wani wurin kuma ya fada, yana mai razanarwa, yace:

“Ya Allah, ni na barranta kuma babu ruwana da masu tozarta hakkin mutum biyu: maraya da mace.” [Ibnu Majah]

Idan kuma mace taki mijin ta, wato ta ji cewa ba zata iya cigaba da rayuwa da shi ba, to Musulunci ya bata damar neman rabuwa ta hanyar yin khul’i, wato fita daga karkashin ikon shi. Ibnu Abbas (RA) ya ruwaito cewa:

“Matar Thabit Dan Kais ta zo wurin Manzon Allah (SAW) sai tace: “Ya Manzon Allah, ni bana kin Thabit saboda addinin shi ko dabi’un shi, sai dai ni ina jin tsoron yin kafirci! (ma’ana aibata halittar shi ko yin butulci).” Sai Manzon Allah yace: “Shin zaki mayar masa da gonar shi (wadda ya bayar a matsayin sadaki)?” tace: “Eh.” Sai ta mayar masa da gonar shi, sai Manzon Allah ya umarce shi da ya sawwake mata.” [Bukhari]

Kamar yadda Annabi (SAW) ya tabbatar wa da mace cewa tana da ‘yancin mallakar kudi kamar kowane da namiji. Sannan tana da damar saye da sayarwa. Zata iya amsar haya, a bata haya, za’a iya sanya ta wakilci, za’a bata kyauta, babu wata katanga a kanta, matukar dai baliga ce kuma shiryayya, duba da fadin Allah (SWT) a inda yace:

“To, idan kun lura da shiriya daga gare su, to, ku mika masu
dukiyoyin su.” [Suratun Nisa’i, aya ta 6]

A lokacin da Ummu Hani ta bai wa Mushrikai biyu mafaka, sai mijinta ya dage cewa sai ya kashe su, saboda yana ganin cewa ita mace ce, a ganin sa kuma mace bata isa ta bayar da mafaka ba. Sai Manzon Allah (SAW) yayi hukunci da cewa:

“Hakika mun ba da mafaka ga wanda kika ba mafaka ya Ummu Hani.” [Bukhari]

Anan, sai Annabi (SAW) ya bata damar ta bada mafaka da aminci a lokacin zaman lafiya ko lokacin yaki ga wanda ba Musulmi ba.

Ya ku al’ummah, kamar haka ne fa mace Musulma take gudanar da rayuwa madaukakiya a cikin al’ummah, karkashin karantarwar addinin Musulunci mai cike da adalci. Ba kamar yadda yawanci a yau ake kokarin danne wa mace hakkinta ba, tare da cutar da ita. Lallai ya zama dole, ya zama tilas, kuma ya zama wajibi mu sake yin bitar hakkin mata a cikin koyarwar addinin Musulunci, domin rashin yin hakan yana kokarin jawo wa matan Musulmi matsala, musamman a kasar hausa, ko in ce a arewacin Najeriya. Ta yadda hatta ilimin da yake dole kuma wajibi ga mace da namiji, yawancin mu bamu bari ‘ya’yan mu mata suyi, saboda zalunci da rashin fahimtar addini.

Ya ku jama’ah, irin fa wannan gwagwarmayar ta kwato hakkin mata da addininmu na Musulunci ya basu, amma wasu azzalumai daga cikin maza suke kokarin danne masu, shine aikin da Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II yayi yunkurin yi shi da wasu jajirtattun malamai, marasa tsoro, amma sai aka wayi gari wasu jahilai suka kasa fahimtar su, saboda sun fi so a kyale su su ci gaba da danne hakkin matayensu.

Ina rokon Allah yasa mu gane, amin.

Dan uwanku, Imam Murtadha Muhammad Gusau ne ya rubuta daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaHausaLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Za a gina cibiyar koya wa masu digiri da difiloma sabbin dabarun fiɗar shanu, tumaki da awaki

Next Post

KORONA: Mutum 152 suka kamu a Najeriya ranar Lahadi

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
RAHOTO: Yadda rashin jin dandano da kamshi abinci ke tsorata ‘yan Najeriya, “Ko mun kamu da Korona ne”?

KORONA: Mutum 152 suka kamu a Najeriya ranar Lahadi

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Ramalan Yero ya fice daga PDP, ya ce jam’iyyar ta ishe shi haka nan
  • Ba za mu bari a yi mana rinto da rana tsaka ba, mutanen Kaduna mu suka zaɓa – Ashiru
  • TATTALIN ARZIKI: Gwamnatin Tarayya ta tara naira tiriliyan 10.18 a 2022
  • KURUNKUS: Kwamitin Amintattun jam’iyyar NNPP sun kori Kwankwaso daga Jam’iyyar Kwatakwata
  • Kotu ta ci tarar gwamnatin Kano Naira biliyan 30 saboda rusa ginegine ba bisa ka’ida ba

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.